• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Sace Amarya Da Dalibi A Katsina

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Lauya A Zamfara

'Yan Bindiga

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu ‘yan bindiga sun kai farmaki rukunin wasu gidaje a Dutsen Reme a karamar hukumar Bakori ta Jihar Katsina tare da yin garkuwa da mutane hudu.

Lamarin dai a cewar mazauna yankin ya faru ne da misalin karfe 10:00 na daren ranar Juma’a.

  • Manufarmu Tsaftace Sana’ar Dirama A Fadin Kasar Nan -Umar Gobir
  • Sassauta Matakan Kandagarkin Cutar COVID-19 A Amurka Ya Haifar Da Mumunan Tasiri

A cewar wani Ahmed Ridwan, mazaunin Dutsen Reme, maharan sun yi amfani da ruwan sama kuma suka aiwatar da aikinsu ba tare da wata matsala ba.

“Mutanen kauye da ke kusa da Maska ne suka sanar da mu ta wayar tarho cewa ‘yan bindiga da dama sun nufo unguwarmu kuma nan take muka sanar da ‘yan sanda da sojoji. Amma da suka isa, tuni ‘yan bindigar sun yi awon gaba da mutane hudu,” in ji Ridwan.

Malam Lawal Hamisu Maska, wanda ba ya nan a lokacin da ‘yan bindigar suka kai farmaki gidansu, ya ce an sace ma’aikacin babbar kotun Funtuwa mai suna Bishir Shitu Sallau tare da wani Safiyanu, dalibin Kwalejin Ilimi da ke Abuja.

Labarai Masu Nasaba

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

Ya ce, “Ba na nan lokacin da ’yan bindigar suka shiga gidanmu; Tuni Bishir da Safiyanu suka boye matansu a bandaki, sai da ‘yan bindigar suka fasa kofar suka nemi matan amma ba su gansu ba. Don haka suka tafi da mazajensu.”

A dalilin faruwar lamarin, Hamisu Maska ya ce zai tashi daga gidansa da kuma unguwar domin neman mafaka.

“Ni likita ne kuma aikina ne ya kawo ni Funtuwa daga Maska. Wannan rashin tsaro da ba ba zai bari na yi aikina yadda ya kamata ba,” inji shi.

A wajen aikin ne suka yi awon gaba da wata Lauratu Jibril da diyarta, bayan da mijinta Malam Jibril ya tsira da kyar.

Wata kanwar wanda aka kashe, Safarau Sanusi, ta ce ‘yan bindigar sun shiga yankin da misalin karfe 9:45 na dare.

“Lauratu sabuwar amarya ce, ba ta wuce kwana 30 a gidan miji ba kafin a sace ta. Lokacin da mijin ya ga ba haza, sai ya yi sauri ya tsere,” in ji ta.

A cewar mazauna garin kwanaki bakwai da suka gabata ‘yan bindigar sun yi garkuwa da mutane biyu a wani gida.

Hakazalika, a makon da ya gabata, an sace wani Tajuddeen, mai gyaran taya, da matar wani Tanimu Mohammed da ke Unguwar Maitandama.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmaryaDalibiKatsinaLikitaMa'aikataRashin Tsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wang Yi Ya Gana Da Jakadan Rasha A Sin Mai Barin Gado

Next Post

EFCC Ta Sallami Kakakin Dokokin Ogun Bayan Shan Tambayoyi Kan Zargin Sama Da Fadi

Related

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

5 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

1 day ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

1 day ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

1 day ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

1 day ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

2 days ago
Next Post
2023: Ba Za Mu Zabi Shugaban Da Ba Zai Mayar Da Hankali Kan Hakkokinmu Ba —’Yan Fansho

EFCC Ta Sallami Kakakin Dokokin Ogun Bayan Shan Tambayoyi Kan Zargin Sama Da Fadi

LABARAI MASU NASABA

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.