• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Sace Amarya Da Dalibi A Katsina

by Sadiq
3 years ago
'Yan Bindiga

'Yan Bindiga

Wasu ‘yan bindiga sun kai farmaki rukunin wasu gidaje a Dutsen Reme a karamar hukumar Bakori ta Jihar Katsina tare da yin garkuwa da mutane hudu.

Lamarin dai a cewar mazauna yankin ya faru ne da misalin karfe 10:00 na daren ranar Juma’a.

  • Manufarmu Tsaftace Sana’ar Dirama A Fadin Kasar Nan -Umar Gobir
  • Sassauta Matakan Kandagarkin Cutar COVID-19 A Amurka Ya Haifar Da Mumunan Tasiri

A cewar wani Ahmed Ridwan, mazaunin Dutsen Reme, maharan sun yi amfani da ruwan sama kuma suka aiwatar da aikinsu ba tare da wata matsala ba.

“Mutanen kauye da ke kusa da Maska ne suka sanar da mu ta wayar tarho cewa ‘yan bindiga da dama sun nufo unguwarmu kuma nan take muka sanar da ‘yan sanda da sojoji. Amma da suka isa, tuni ‘yan bindigar sun yi awon gaba da mutane hudu,” in ji Ridwan.

Malam Lawal Hamisu Maska, wanda ba ya nan a lokacin da ‘yan bindigar suka kai farmaki gidansu, ya ce an sace ma’aikacin babbar kotun Funtuwa mai suna Bishir Shitu Sallau tare da wani Safiyanu, dalibin Kwalejin Ilimi da ke Abuja.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Ya ce, “Ba na nan lokacin da ’yan bindigar suka shiga gidanmu; Tuni Bishir da Safiyanu suka boye matansu a bandaki, sai da ‘yan bindigar suka fasa kofar suka nemi matan amma ba su gansu ba. Don haka suka tafi da mazajensu.”

A dalilin faruwar lamarin, Hamisu Maska ya ce zai tashi daga gidansa da kuma unguwar domin neman mafaka.

“Ni likita ne kuma aikina ne ya kawo ni Funtuwa daga Maska. Wannan rashin tsaro da ba ba zai bari na yi aikina yadda ya kamata ba,” inji shi.

A wajen aikin ne suka yi awon gaba da wata Lauratu Jibril da diyarta, bayan da mijinta Malam Jibril ya tsira da kyar.

Wata kanwar wanda aka kashe, Safarau Sanusi, ta ce ‘yan bindigar sun shiga yankin da misalin karfe 9:45 na dare.

“Lauratu sabuwar amarya ce, ba ta wuce kwana 30 a gidan miji ba kafin a sace ta. Lokacin da mijin ya ga ba haza, sai ya yi sauri ya tsere,” in ji ta.

A cewar mazauna garin kwanaki bakwai da suka gabata ‘yan bindigar sun yi garkuwa da mutane biyu a wani gida.

Hakazalika, a makon da ya gabata, an sace wani Tajuddeen, mai gyaran taya, da matar wani Tanimu Mohammed da ke Unguwar Maitandama.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 
Manyan Labarai

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama
Manyan Labarai

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025
Next Post
2023: Ba Za Mu Zabi Shugaban Da Ba Zai Mayar Da Hankali Kan Hakkokinmu Ba —’Yan Fansho

EFCC Ta Sallami Kakakin Dokokin Ogun Bayan Shan Tambayoyi Kan Zargin Sama Da Fadi

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

November 6, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.