ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Sace Amarya Da Dalibi A Katsina

by Sadiq
4 years ago
'Yan Bindiga

'Yan Bindiga

Wasu ‘yan bindiga sun kai farmaki rukunin wasu gidaje a Dutsen Reme a karamar hukumar Bakori ta Jihar Katsina tare da yin garkuwa da mutane hudu.

Lamarin dai a cewar mazauna yankin ya faru ne da misalin karfe 10:00 na daren ranar Juma’a.

  • Manufarmu Tsaftace Sana’ar Dirama A Fadin Kasar Nan -Umar Gobir
  • Sassauta Matakan Kandagarkin Cutar COVID-19 A Amurka Ya Haifar Da Mumunan Tasiri

A cewar wani Ahmed Ridwan, mazaunin Dutsen Reme, maharan sun yi amfani da ruwan sama kuma suka aiwatar da aikinsu ba tare da wata matsala ba.

ADVERTISEMENT

“Mutanen kauye da ke kusa da Maska ne suka sanar da mu ta wayar tarho cewa ‘yan bindiga da dama sun nufo unguwarmu kuma nan take muka sanar da ‘yan sanda da sojoji. Amma da suka isa, tuni ‘yan bindigar sun yi awon gaba da mutane hudu,” in ji Ridwan.

Malam Lawal Hamisu Maska, wanda ba ya nan a lokacin da ‘yan bindigar suka kai farmaki gidansu, ya ce an sace ma’aikacin babbar kotun Funtuwa mai suna Bishir Shitu Sallau tare da wani Safiyanu, dalibin Kwalejin Ilimi da ke Abuja.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Ya ce, “Ba na nan lokacin da ’yan bindigar suka shiga gidanmu; Tuni Bishir da Safiyanu suka boye matansu a bandaki, sai da ‘yan bindigar suka fasa kofar suka nemi matan amma ba su gansu ba. Don haka suka tafi da mazajensu.”

A dalilin faruwar lamarin, Hamisu Maska ya ce zai tashi daga gidansa da kuma unguwar domin neman mafaka.

“Ni likita ne kuma aikina ne ya kawo ni Funtuwa daga Maska. Wannan rashin tsaro da ba ba zai bari na yi aikina yadda ya kamata ba,” inji shi.

A wajen aikin ne suka yi awon gaba da wata Lauratu Jibril da diyarta, bayan da mijinta Malam Jibril ya tsira da kyar.

Wata kanwar wanda aka kashe, Safarau Sanusi, ta ce ‘yan bindigar sun shiga yankin da misalin karfe 9:45 na dare.

“Lauratu sabuwar amarya ce, ba ta wuce kwana 30 a gidan miji ba kafin a sace ta. Lokacin da mijin ya ga ba haza, sai ya yi sauri ya tsere,” in ji ta.

A cewar mazauna garin kwanaki bakwai da suka gabata ‘yan bindigar sun yi garkuwa da mutane biyu a wani gida.

Hakazalika, a makon da ya gabata, an sace wani Tajuddeen, mai gyaran taya, da matar wani Tanimu Mohammed da ke Unguwar Maitandama.

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
2023: Ba Za Mu Zabi Shugaban Da Ba Zai Mayar Da Hankali Kan Hakkokinmu Ba —’Yan Fansho

EFCC Ta Sallami Kakakin Dokokin Ogun Bayan Shan Tambayoyi Kan Zargin Sama Da Fadi

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.