ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Sace Amarya Da Dalibi A Katsina

by Sadiq
4 years ago
'Yan Bindiga

'Yan Bindiga

Wasu ‘yan bindiga sun kai farmaki rukunin wasu gidaje a Dutsen Reme a karamar hukumar Bakori ta Jihar Katsina tare da yin garkuwa da mutane hudu.

Lamarin dai a cewar mazauna yankin ya faru ne da misalin karfe 10:00 na daren ranar Juma’a.

  • Manufarmu Tsaftace Sana’ar Dirama A Fadin Kasar Nan -Umar Gobir
  • Sassauta Matakan Kandagarkin Cutar COVID-19 A Amurka Ya Haifar Da Mumunan Tasiri

A cewar wani Ahmed Ridwan, mazaunin Dutsen Reme, maharan sun yi amfani da ruwan sama kuma suka aiwatar da aikinsu ba tare da wata matsala ba.

ADVERTISEMENT

“Mutanen kauye da ke kusa da Maska ne suka sanar da mu ta wayar tarho cewa ‘yan bindiga da dama sun nufo unguwarmu kuma nan take muka sanar da ‘yan sanda da sojoji. Amma da suka isa, tuni ‘yan bindigar sun yi awon gaba da mutane hudu,” in ji Ridwan.

Malam Lawal Hamisu Maska, wanda ba ya nan a lokacin da ‘yan bindigar suka kai farmaki gidansu, ya ce an sace ma’aikacin babbar kotun Funtuwa mai suna Bishir Shitu Sallau tare da wani Safiyanu, dalibin Kwalejin Ilimi da ke Abuja.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ya ce, “Ba na nan lokacin da ’yan bindigar suka shiga gidanmu; Tuni Bishir da Safiyanu suka boye matansu a bandaki, sai da ‘yan bindigar suka fasa kofar suka nemi matan amma ba su gansu ba. Don haka suka tafi da mazajensu.”

A dalilin faruwar lamarin, Hamisu Maska ya ce zai tashi daga gidansa da kuma unguwar domin neman mafaka.

“Ni likita ne kuma aikina ne ya kawo ni Funtuwa daga Maska. Wannan rashin tsaro da ba ba zai bari na yi aikina yadda ya kamata ba,” inji shi.

A wajen aikin ne suka yi awon gaba da wata Lauratu Jibril da diyarta, bayan da mijinta Malam Jibril ya tsira da kyar.

Wata kanwar wanda aka kashe, Safarau Sanusi, ta ce ‘yan bindigar sun shiga yankin da misalin karfe 9:45 na dare.

“Lauratu sabuwar amarya ce, ba ta wuce kwana 30 a gidan miji ba kafin a sace ta. Lokacin da mijin ya ga ba haza, sai ya yi sauri ya tsere,” in ji ta.

A cewar mazauna garin kwanaki bakwai da suka gabata ‘yan bindigar sun yi garkuwa da mutane biyu a wani gida.

Hakazalika, a makon da ya gabata, an sace wani Tajuddeen, mai gyaran taya, da matar wani Tanimu Mohammed da ke Unguwar Maitandama.

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
2023: Ba Za Mu Zabi Shugaban Da Ba Zai Mayar Da Hankali Kan Hakkokinmu Ba —’Yan Fansho

EFCC Ta Sallami Kakakin Dokokin Ogun Bayan Shan Tambayoyi Kan Zargin Sama Da Fadi

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.