‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mutum 16 a Æ™auyen Mararraba Mazuga da ke Æ™aramar hukumar Kachia a Jihar Kaduna.Â
Lamarin ya faru tsakanin ƙarfe 11 na daren ranar Alhamis zuwa ƙarfe 12 na safiyar Juma’a.
- Gwamna Sule Ya Rushe Majalisar Zartarwar Nasarawa, Ya Sauke Sakataren Gwamnati
- Tabbas Sin Za Ta Ci Gaba Da Jan Zarenta A 2025
Mutum biyu sun tsere daga hannun maharan, yayin da aka saki mutum bakwai don su nemo kuÉ—in fansar sauran mutanen da suka kama.
Daga cikin waÉ—anda ke tsare akwai ‘ya’ya biyu na wata mata mai suna Na’omi Kayit, sai mutum É—aya daga cikin waÉ—anda aka saki.
ÆŠaya daga cikin ‘ya’yan naga É—aliba ce a ABU Zariya, yayin da É—ayar ke karatu a Togo.
Har yanzu, masu garkuwa da mutanen ba su tuntuɓi iyalan waɗanda suka kama don neman kuɗin fansa ba.
ƘoÆ™arin jin ta bakin rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna bai yi nasara ba, domin ba a samu kakakin rundunar ba, ASP Munsir Hassan.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp