• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Mutan 3 Yankan Rago Da Sace Wasu Da Dama A Wani Sabon Hari A Neja

A yayin harin, kimanin mutane uku ne suka rasa rayukansu, sannan an sace wasu da ba a tantance adadinsu ba, yayin da aka kona gidaje biyu.

by Muhammad
3 years ago
in Labarai
0
‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Mutan 3 Yankan Rago Da Sace Wasu Da Dama A Wani Sabon Hari A Neja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An yi wa mutane uku yankan rago yayin da aka yi garkuwa da wasu da ba a tantance adadinsu ba a daren Laraba a unguwar Maguzawa da ke karamar hukumar Rafi a jihar Neja.

Rahotanni da dama daga yankin sun ce daga cikin wadanda aka sace akwai mata da kananan yara yayin da mazauna yankin da dama suka tsere daga gidajensu zuwa Kagara da Pandogari a jihar Neja da kuma garin Birnin Gwari a jihar Kaduna.

  • ‘Yan bindiga Sun Kai Hari Kauyuka 8 Da Kashe 33 Da Sace Mutum 30 Da Shanu 2,000 A Kebbi Da Neja,
  • ‘Yan Boko Haram 204 Sun Mika Wuya Ga Sojoji A Jihar Borno

Maguzawa dai yana da tazarar kilomita 25 daga garin Kagara a jihar Neja da kuma kilomita 12 daga Birnin Gwari a jihar Kaduna.

Hare-haren na Maguzawa ya zo ne kasa da sa’o’i 48 a lokacin da ‘yan bindiga suka kai wani hari a kauyen Gidigore da ke karamar hukumar Rafi, a daren ranar Talata, inda aka kashe akalla rayuka biyar tare da sace wasu da dama.

Wata majiya da ta nemi a sakaya sunanta ta ce, “A Maguzawa, an kashe mutane uku tare da yin garkuwa da wasu da ba a tantance adadinsu ba, wasu kuma sun gudu. Ya zuwa yanzu mun ga gawarwaki uku da aka yanka su. Ba mu san adadin mutanen da suka tafi tare da su ba a yanzu. ”

Labarai Masu Nasaba

Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari

NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya

Mazauna yankin sun shaida cewa, makwanni uku da suka gabata an yi garkuwa da wasu a karamar hukumar Rafi da da yi musu fashi.

Wani mazaunin garin Ibrahim Ahmad ya ce dan uwansa na daga cikin wadanda aka yi garkuwa da su a daren ranar Talata, inda ya ce mutane da dama sun tsere daga gidajensu zuwa Kagara da Pandogari a jihar Neja da kuma kona Gwari a jihar Kaduna.

“A cikin kasa da makonni uku, mun ga hare-hare daban-daban har guda 10 a kan mutane daban-daban a karamar hukumar Rafi, kusan kowace rana.

Kafin harin na ranar Talata, makonni biyu da suka gabata, ‘yan bindiga sun kai hari a kauyukan Gulbi, Unguwan-Jaye da Kusherki inda aka kashe mutane 8 tare da yin garkuwa da wasu 36 yayin da mutum daya da ya samu munanan raunuka. A yayin da nake magana da ku, sun bukaci Naira miliyan 50 ga mutanen farko da suka yi garkuwa da su,” inji shi.

Ahmad ya ce an kona gidaje da kadarori na manoma da dama a harin na ranar Talata wanda ya dauki sa’o’i da dama.

Ya bukaci tallafin jin kai daga gwamnati, kungiyoyi da daidaikun jama’a musamman kayan abinci da yara kan sanyawa don rage musu kuncin rayuwa.

Al’umar Gidigore da aka kai harin na baya-bayan nan na da tazarar kilomita kadan daga garin Birnin Gwari na jihar Kaduna, inda ‘yan bindigar suka kai hare-hare da dama.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Neja, DSP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar harin na Didigore amma har yanzu bai tabbatar da sabon harin ba.

Ya ce, “A yayin harin, kimanin mutane uku ne suka rasa rayukansu, sannan an sace wasu da ba a tantance adadinsu ba, yayin da aka kona gidaje biyu.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NejaYan bindigaYankan Rago
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan bindiga Sun Kai Hari Kauyuka 8 Da Kashe 33 Da Sace Mutum 30 Da Shanu 2,000 A Kebbi Da Neja,

Next Post

2023: Atiku Ya Gabatar Da Gwamnan Delta, Okowa A Matsayin Mataimakinsa

Related

Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari
Labarai

Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari

5 minutes ago
NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya
Labarai

NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya

1 hour ago
Neja: Cikin Wata 10 Ibtila’i Ya Lakume Rayuka Sama Da 400 – NSMA
Labarai

Neja: Cikin Wata 10 Ibtila’i Ya Lakume Rayuka Sama Da 400 – NSMA

2 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

3 hours ago
Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

4 hours ago
Ba A Taɓa Nuno Bidiyon Shugaban Jam’iyyarmu Ta ADC Yana Cusa Dala A Aljihu Ba —Dalung
Labarai

Ba A Taɓa Nuno Bidiyon Shugaban Jam’iyyarmu Ta ADC Yana Cusa Dala A Aljihu Ba —Dalung

4 hours ago
Next Post
Sun

2023: Atiku Ya Gabatar Da Gwamnan Delta, Okowa A Matsayin Mataimakinsa

LABARAI MASU NASABA

Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari

Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari

July 4, 2025
Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus

Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus

July 4, 2025
NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya

NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya

July 4, 2025
Neja: Cikin Wata 10 Ibtila’i Ya Lakume Rayuka Sama Da 400 – NSMA

Neja: Cikin Wata 10 Ibtila’i Ya Lakume Rayuka Sama Da 400 – NSMA

July 4, 2025
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

July 4, 2025

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

July 4, 2025
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

July 4, 2025
Ba A Taɓa Nuno Bidiyon Shugaban Jam’iyyarmu Ta ADC Yana Cusa Dala A Aljihu Ba —Dalung

Ba A Taɓa Nuno Bidiyon Shugaban Jam’iyyarmu Ta ADC Yana Cusa Dala A Aljihu Ba —Dalung

July 4, 2025
Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447: Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (1)

Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447: Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (1)

July 4, 2025
Ayyukan ‘Yan Ta’adda Na Barazana Ga Shirin Gwamnati Na Wadata Kasa Da Abinci

Ayyukan ‘Yan Ta’adda Na Barazana Ga Shirin Gwamnati Na Wadata Kasa Da Abinci

July 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.