ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, September 19, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Mutan 3 Yankan Rago Da Sace Wasu Da Dama A Wani Sabon Hari A Neja

A yayin harin, kimanin mutane uku ne suka rasa rayukansu, sannan an sace wasu da ba a tantance adadinsu ba, yayin da aka kona gidaje biyu.

by Muhammad
4 years ago
Sun

An yi wa mutane uku yankan rago yayin da aka yi garkuwa da wasu da ba a tantance adadinsu ba a daren Laraba a unguwar Maguzawa da ke karamar hukumar Rafi a jihar Neja.

Rahotanni da dama daga yankin sun ce daga cikin wadanda aka sace akwai mata da kananan yara yayin da mazauna yankin da dama suka tsere daga gidajensu zuwa Kagara da Pandogari a jihar Neja da kuma garin Birnin Gwari a jihar Kaduna.

  • ‘Yan bindiga Sun Kai Hari Kauyuka 8 Da Kashe 33 Da Sace Mutum 30 Da Shanu 2,000 A Kebbi Da Neja,
  • ‘Yan Boko Haram 204 Sun Mika Wuya Ga Sojoji A Jihar Borno

Maguzawa dai yana da tazarar kilomita 25 daga garin Kagara a jihar Neja da kuma kilomita 12 daga Birnin Gwari a jihar Kaduna.

ADVERTISEMENT

Hare-haren na Maguzawa ya zo ne kasa da sa’o’i 48 a lokacin da ‘yan bindiga suka kai wani hari a kauyen Gidigore da ke karamar hukumar Rafi, a daren ranar Talata, inda aka kashe akalla rayuka biyar tare da sace wasu da dama.

Wata majiya da ta nemi a sakaya sunanta ta ce, “A Maguzawa, an kashe mutane uku tare da yin garkuwa da wasu da ba a tantance adadinsu ba, wasu kuma sun gudu. Ya zuwa yanzu mun ga gawarwaki uku da aka yanka su. Ba mu san adadin mutanen da suka tafi tare da su ba a yanzu. ”

LABARAI MASU NASABA

Trump Ya Hana CNN Da Wasu Kafofin Yaɗa Labarai Shiga Fadar White House

Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Bauchi Ta Yi Allah-wadai Da Kama Masu Kaɗa Ƙuri’a

Mazauna yankin sun shaida cewa, makwanni uku da suka gabata an yi garkuwa da wasu a karamar hukumar Rafi da da yi musu fashi.

Wani mazaunin garin Ibrahim Ahmad ya ce dan uwansa na daga cikin wadanda aka yi garkuwa da su a daren ranar Talata, inda ya ce mutane da dama sun tsere daga gidajensu zuwa Kagara da Pandogari a jihar Neja da kuma kona Gwari a jihar Kaduna.

“A cikin kasa da makonni uku, mun ga hare-hare daban-daban har guda 10 a kan mutane daban-daban a karamar hukumar Rafi, kusan kowace rana.

Kafin harin na ranar Talata, makonni biyu da suka gabata, ‘yan bindiga sun kai hari a kauyukan Gulbi, Unguwan-Jaye da Kusherki inda aka kashe mutane 8 tare da yin garkuwa da wasu 36 yayin da mutum daya da ya samu munanan raunuka. A yayin da nake magana da ku, sun bukaci Naira miliyan 50 ga mutanen farko da suka yi garkuwa da su,” inji shi.

Ahmad ya ce an kona gidaje da kadarori na manoma da dama a harin na ranar Talata wanda ya dauki sa’o’i da dama.

Ya bukaci tallafin jin kai daga gwamnati, kungiyoyi da daidaikun jama’a musamman kayan abinci da yara kan sanyawa don rage musu kuncin rayuwa.

Al’umar Gidigore da aka kai harin na baya-bayan nan na da tazarar kilomita kadan daga garin Birnin Gwari na jihar Kaduna, inda ‘yan bindigar suka kai hare-hare da dama.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Neja, DSP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar harin na Didigore amma har yanzu bai tabbatar da sabon harin ba.

Ya ce, “A yayin harin, kimanin mutane uku ne suka rasa rayukansu, sannan an sace wasu da ba a tantance adadinsu ba, yayin da aka kona gidaje biyu.”

Sun
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu
  • Muhammad
    Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
  • Muhammad
    An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
  • Muhammad
    Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano

MASU ALAKA

Trump Ya Hana CNN Da Wasu Kafofin Yaɗa Labarai Shiga Fadar White House
Kasashen Ketare

Trump Ya Hana CNN Da Wasu Kafofin Yaɗa Labarai Shiga Fadar White House

September 19, 2026
Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Bauchi Ta Yi Allah-wadai Da Kama Masu Kaɗa Ƙuri’a
Labarai

Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Bauchi Ta Yi Allah-wadai Da Kama Masu Kaɗa Ƙuri’a

September 19, 2026
Kungiyar ’Yan Kasuwar Kaduna Ta Rantsar Da Sabon Shugaban Riƙo
Labarai

Kungiyar ’Yan Kasuwar Kaduna Ta Rantsar Da Sabon Shugaban Riƙo

September 19, 2026
Next Post
Sun

2023: Atiku Ya Gabatar Da Gwamnan Delta, Okowa A Matsayin Mataimakinsa

LABARAI MASU NASABA

Trump Ya Hana CNN Da Wasu Kafofin Yaɗa Labarai Shiga Fadar White House

Trump Ya Hana CNN Da Wasu Kafofin Yaɗa Labarai Shiga Fadar White House

September 19, 2026
Adadin Tafiye-Tafiyen Da Jiragen Kasa Masu Jigilar Fasinjoji Suka Yi A Sin Ya Kai Matsayin Koli A Watanni 8 Na Bana

Adadin Tafiye-Tafiyen Da Jiragen Kasa Masu Jigilar Fasinjoji Suka Yi A Sin Ya Kai Matsayin Koli A Watanni 8 Na Bana

September 19, 2026
Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Bauchi Ta Yi Allah-wadai Da Kama Masu Kaɗa Ƙuri’a

Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Bauchi Ta Yi Allah-wadai Da Kama Masu Kaɗa Ƙuri’a

September 19, 2026
Kungiyar ’Yan Kasuwar Kaduna Ta Rantsar Da Sabon Shugaban Riƙo

Kungiyar ’Yan Kasuwar Kaduna Ta Rantsar Da Sabon Shugaban Riƙo

September 19, 2026
Sin Na Fatan Inganta Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya Na MDD

Sin Na Fatan Inganta Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya Na MDD

September 19, 2026
Rikicin Fili: Harsashi Ya Yi Ajalin Ɗalibin Jami’a A Neja

Rikicin Fili: Harsashi Ya Yi Ajalin Ɗalibin Jami’a A Neja

September 19, 2026
An Gudanar Da Jerin Shirye Shiryen Gabatar Da Al’adun Kasar Sin A WTO

An Gudanar Da Jerin Shirye Shiryen Gabatar Da Al’adun Kasar Sin A WTO

September 19, 2026
Za A Gudanar Da Shawarwari Tsakanin Sin Da Amurka Kan Tattalin Arziki Da Cinikayya

Za A Gudanar Da Shawarwari Tsakanin Sin Da Amurka Kan Tattalin Arziki Da Cinikayya

September 19, 2026
Motoci Masu Amfani Da CNG Da Lantarki Sun Rage Kuɗin Sufuri Da Kashi 83 – Tinubu

Motoci Masu Amfani Da CNG Da Lantarki Sun Rage Kuɗin Sufuri Da Kashi 83 – Tinubu

September 19, 2026
Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Angola: Kasar Sin Tana Da Shugaba Mai Hangen Nesa

Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Angola: Kasar Sin Tana Da Shugaba Mai Hangen Nesa

September 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.