• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Zame Wa Manoma Karfen Kafa

by Abubakar Abba
3 years ago
in Noma Da Kiwo
0
‘Yan Bindiga Sun Zame Wa Manoma Karfen Kafa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan bindiga sun addabi dubban manoma a jihar Taraba, inda hakan ya hana su zuwa gonakinsu domin yin noma, hakan ya kuma hana kusan al’ummomi 20 da ke yin noma a yankuna daban-daban yin noma.

An ruwaito cewa, ‘yan bidigar sun hakan manoman zuwa gonakinsu kamar wadanda ke yankin Gassol da ke a cikin karamar hukumar Bali, inda suka yi barazanar kashe duk manomin da suka samu ya je gona domin yin noma.

  • Yadda Zamfarawa Suka Karbi Tuban Kasurgumin Dan Bindiga Bello Turji

Lamarin sai kara munana yake yi a yankunan a kullum, inda kuma aka ruwaito cewa, ‘yan bindigar sun sace wasu manoman da kuma masu kiwon shanu, inda lamarin ya tilasta su yin hijira zuwa Jalingo, Tella da Mutumbiyu.

An ruwaito cewa, a cikin makwannon da suka gabata, ‘yan bindigar sun yi garkuwa da sama da manoma 50, inda kuma suka bukaci a basu kudin fansa daga naira miliyan 5 zuwa naira miliyan 7 a kan ko wanne manomi daya, kafin su sako su.

Akasarin wadanda lamarin ya rutsa da su, ya tilasta masu sayar da kadarorin su domin su biya ‘yan bindigar kudaden fansa.

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Wani bincike ya nuna cewa, ‘yan bindir na dorawa wasu manoman haraji kafin su bar su suje gonakan su domin noma su.
‘Yan bindigar wadanda ke zuwa a kan baburansu, sun kuma tarwatsa mazauna yankunan Jauro Manu da BabaJoli da Garin da Gidado da Anema da kuma wadanda ke da zama a kauyukan da ke karamar Bali.

Sauran al’umomin da ke ci gaba da fuskantar barazanar ta ‘yan bindiga a jihar sun hada da, Baba Also da Adamu Ja da Garin Simaila da Nabayi da garin Karfe da Yola Karejo da Garin Gaga, Yarima da TibKwayo da Kumburo da Wayo Kwayosa da Gidan Iro da kuma Gidan Jafala.

Tuni dai, manoman da ke wadannan yankunan suka kaurace wa gonakansu da kuma amfanin gona da suka shuka.
Daya daga cikin manoman wanda bai bukaci a ambaci sunansa wanda kuma shi ma, ‘yan bindigar suka taba sace wa, ya bayyana cewa, sau uku ana yin garkuwa da shi, inda sai da ya biya kudin fansa naira miliyan 5.4 kafin a sako shi.
An ruwaito cewa, hatta masu rike da mukaman gargajiya wasu yankunan jihar sum aba su tsira daga sacewar da ‘ yan bindigar ke yi masu ba, inda har ta kai ga, sun sace Dagatan kauyukan Maigemu, Maisamari da kuma na Garing Barau suka kuma kashe su.

Sun kuma sace Dagacin kauyen Gunduma, Mallam Wali Gunduma, amma daga baya suka sako shi bayan an biysa su kudin fansa.

‘Yan bindigar sun kuma hana manoman da ke a yankunan zuwa noma gonakansu a kakar noman bana.
An ruwaito cewa, sama da kashi 70 na jimlar Shinkafar da Masara da Gyada da sauran amfanin gona, da ke noma da kuma m wa jihar Taraba na fitowa ne daga Bali da kuma Gassol.

Wani mazaunin yankin ya bayyana cewa, “ Muna noma manyan amfanin gona da suka hada da, Shinkafa ‘yar gida, Gyada da sauran amfanin gona, amma a yanzu, ‘yan bindigar sun karbe akasarin gonakan da ake noma wa a yankunan , inda ya kara da cewa, hakan ya janyo aikin noma ya ragu matuka a yankunan jihar”.

Wani mai sana’ar sayar da Shanu a jihar Alhaji Boshe ya sanar da cewa, sau hudu masu garkuwar suna sace shi kuma a duk lokacin da suka sace shi, sai ya biya kimanin naira miliyan 5 kudin fansa kafin su sako shi.

Alhaji Boshe ya kara da cewa, lokacin da suka sace shi a watan da ya gabata, sai da ‘yan uwansa suka ranto naira miliyan 5.5 kudin fansa tare da biyan kudin ruwa domin a sako shi.

A cewar Boshe, akasarin Fulani Makiyaya a wasu yankunan da ke a jihar, suka sayar da kimain shanu 300 saboda biyan kudin fansa ga ‘yan bindigar kafin su sako su.

Ya kara da cewa, saboda barazanar masu garkuwar, Fulani Makiyya da dama sun ta shi daga matsugunan su, inda ya bayyana cewa, idan har mutum babban manomi ne ko babban mai kiwo a yankunan za ka ci gaba da fuskantar barazanar ta ‘yan bindigar domin ako wanne lokaci, masu kai wa ‘yan bindigar bayanan sirri suna bibiyar manoman da Fulani Makiyyan, musamman idan sun yi wata hada-hadar cinikayya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Goron Juma’a

Next Post

Wariyar Launin Fata Ta Fi Cuta Barna

Related

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

5 hours ago
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya
Noma Da Kiwo

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

13 hours ago
Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji
Noma Da Kiwo

Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

2 days ago
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje
Noma Da Kiwo

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

7 days ago
Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir
Noma Da Kiwo

Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir

1 week ago
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona
Noma Da Kiwo

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

2 weeks ago
Next Post
Wariyar Launin Fata Ta Fi Cuta Barna

Wariyar Launin Fata Ta Fi Cuta Barna

LABARAI MASU NASABA

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

August 10, 2025
Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

August 10, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

August 10, 2025
Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

August 10, 2025
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

August 10, 2025
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

August 9, 2025
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

August 9, 2025
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.