ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Zame Wa Manoma Karfen Kafa

by Abubakar Abba
3 years ago
Bindiga

‘Yan bindiga sun addabi dubban manoma a jihar Taraba, inda hakan ya hana su zuwa gonakinsu domin yin noma, hakan ya kuma hana kusan al’ummomi 20 da ke yin noma a yankuna daban-daban yin noma.

An ruwaito cewa, ‘yan bidigar sun hakan manoman zuwa gonakinsu kamar wadanda ke yankin Gassol da ke a cikin karamar hukumar Bali, inda suka yi barazanar kashe duk manomin da suka samu ya je gona domin yin noma.

  • Yadda Zamfarawa Suka Karbi Tuban Kasurgumin Dan Bindiga Bello Turji

Lamarin sai kara munana yake yi a yankunan a kullum, inda kuma aka ruwaito cewa, ‘yan bindigar sun sace wasu manoman da kuma masu kiwon shanu, inda lamarin ya tilasta su yin hijira zuwa Jalingo, Tella da Mutumbiyu.

ADVERTISEMENT

An ruwaito cewa, a cikin makwannon da suka gabata, ‘yan bindigar sun yi garkuwa da sama da manoma 50, inda kuma suka bukaci a basu kudin fansa daga naira miliyan 5 zuwa naira miliyan 7 a kan ko wanne manomi daya, kafin su sako su.

Akasarin wadanda lamarin ya rutsa da su, ya tilasta masu sayar da kadarorin su domin su biya ‘yan bindigar kudaden fansa.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

Wani bincike ya nuna cewa, ‘yan bindir na dorawa wasu manoman haraji kafin su bar su suje gonakan su domin noma su.
‘Yan bindigar wadanda ke zuwa a kan baburansu, sun kuma tarwatsa mazauna yankunan Jauro Manu da BabaJoli da Garin da Gidado da Anema da kuma wadanda ke da zama a kauyukan da ke karamar Bali.

Sauran al’umomin da ke ci gaba da fuskantar barazanar ta ‘yan bindiga a jihar sun hada da, Baba Also da Adamu Ja da Garin Simaila da Nabayi da garin Karfe da Yola Karejo da Garin Gaga, Yarima da TibKwayo da Kumburo da Wayo Kwayosa da Gidan Iro da kuma Gidan Jafala.

Tuni dai, manoman da ke wadannan yankunan suka kaurace wa gonakansu da kuma amfanin gona da suka shuka.
Daya daga cikin manoman wanda bai bukaci a ambaci sunansa wanda kuma shi ma, ‘yan bindigar suka taba sace wa, ya bayyana cewa, sau uku ana yin garkuwa da shi, inda sai da ya biya kudin fansa naira miliyan 5.4 kafin a sako shi.
An ruwaito cewa, hatta masu rike da mukaman gargajiya wasu yankunan jihar sum aba su tsira daga sacewar da ‘ yan bindigar ke yi masu ba, inda har ta kai ga, sun sace Dagatan kauyukan Maigemu, Maisamari da kuma na Garing Barau suka kuma kashe su.

Sun kuma sace Dagacin kauyen Gunduma, Mallam Wali Gunduma, amma daga baya suka sako shi bayan an biysa su kudin fansa.

‘Yan bindigar sun kuma hana manoman da ke a yankunan zuwa noma gonakansu a kakar noman bana.
An ruwaito cewa, sama da kashi 70 na jimlar Shinkafar da Masara da Gyada da sauran amfanin gona, da ke noma da kuma m wa jihar Taraba na fitowa ne daga Bali da kuma Gassol.

Wani mazaunin yankin ya bayyana cewa, “ Muna noma manyan amfanin gona da suka hada da, Shinkafa ‘yar gida, Gyada da sauran amfanin gona, amma a yanzu, ‘yan bindigar sun karbe akasarin gonakan da ake noma wa a yankunan , inda ya kara da cewa, hakan ya janyo aikin noma ya ragu matuka a yankunan jihar”.

Wani mai sana’ar sayar da Shanu a jihar Alhaji Boshe ya sanar da cewa, sau hudu masu garkuwar suna sace shi kuma a duk lokacin da suka sace shi, sai ya biya kimanin naira miliyan 5 kudin fansa kafin su sako shi.

Alhaji Boshe ya kara da cewa, lokacin da suka sace shi a watan da ya gabata, sai da ‘yan uwansa suka ranto naira miliyan 5.5 kudin fansa tare da biyan kudin ruwa domin a sako shi.

A cewar Boshe, akasarin Fulani Makiyaya a wasu yankunan da ke a jihar, suka sayar da kimain shanu 300 saboda biyan kudin fansa ga ‘yan bindigar kafin su sako su.

Ya kara da cewa, saboda barazanar masu garkuwar, Fulani Makiyya da dama sun ta shi daga matsugunan su, inda ya bayyana cewa, idan har mutum babban manomi ne ko babban mai kiwo a yankunan za ka ci gaba da fuskantar barazanar ta ‘yan bindigar domin ako wanne lokaci, masu kai wa ‘yan bindigar bayanan sirri suna bibiyar manoman da Fulani Makiyyan, musamman idan sun yi wata hada-hadar cinikayya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Noma Da Kiwo

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Next Post
Wariyar Launin Fata Ta Fi Cuta Barna

Wariyar Launin Fata Ta Fi Cuta Barna

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

November 15, 2025
Illolin Neman Kudi Ido Rufe Ba Tare Da Kula Da Halal Ko Haram Ba

Illolin Neman Kudi Ido Rufe Ba Tare Da Kula Da Halal Ko Haram Ba

November 15, 2025
Jakadan Sin A Japan Ya Bayyana Matukar Adawa Da Kalaman Firaminista Takaichi Dangane Da Kasar Sin

Jakadan Sin A Japan Ya Bayyana Matukar Adawa Da Kalaman Firaminista Takaichi Dangane Da Kasar Sin

November 15, 2025
Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
Yadda Ake Miyar Margi (Margi Special)

Yadda Ake Miyar Margi (Margi Special)

November 15, 2025
Yadda Za Ku Gyara Kanku

Yadda Za Ku Gyara Kanku

November 15, 2025
NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

November 15, 2025
Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

November 15, 2025
Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

November 15, 2025
Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.