• English
  • Business News
Thursday, June 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Daba Sun Raunata Soja Da ‘Yan Kwana-Kwana 2 Yayin Da Gobara Ta Tashi A Gidan Mai A Kwara

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
‘Yan Daba Sun Raunata Soja Da ‘Yan Kwana-Kwana 2 Yayin Da Gobara Ta Tashi A Gidan Mai A Kwara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu ‘yan daba sun kai wa wani soja da jami’an kashe gobara biyu na Jihar Kwara hari tare da raunata su yayin da suke aikin ceto a wani gidan mai da gobara ta kone a Ilorin, babban birnin jihar.

An kai sojan da jami’an hukumar kashe gobara ta jihar zuwa gidan man K&R da ke unguwar Oke Agodi a cikin birnin Ilorin, domin kashe wutar da ta tashi da misalin karfe 9:30 na dare.

  • Hisbah Ta Kama Motoci 3 Makare Da Giya A Kano
  • An Cafke Wasu Ma’aurata Kan Zargin Hada Baki Wajen Bizne Jaririyarsu Da Ranta A Jigawa

Amma, ‘yan daban suka fara jifan sojoji da jami’an kashe gobara inda ana haka suka jikkata soja daya da ‘yan kwana-kwana biyu.

LEADERSHIP ta tattaro cewa daga karshe sojojin sun dawo da zaman lafiya a yankin yayin da ‘yan kwana-kwana suka samu nasarar kashe gobarar.

Sai dai gobarar ta cinye motoci biyu da ofisoshi biyu kafin ‘yan kwana-kwana su kashe ta.

Labarai Masu Nasaba

Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci

DHQ Za Ta Tura Dakaru Na Musamman 800 Yankunan Da Ke Fama Da Rashin Tsaro – CDS

Kimanin kadarar Naira 21.7m aka yi asara a gobarar yayin da kiyasin dukiyar da aka ceto daga gobarar ta kai Naira 48.4million.

Kakakin hukumar kashe gobara ta Jihar Kwara, Hassan Adekunle, a wata sanarwa a ranar Laraba, ya tabbatar da barkewar gobarar da harin da aka kai kan sojoji da ‘yan kwana-kwana.

Sanarwar ta kara da cewa: “A jiya Talata 6 ga Disamba, 2022, wasu ‘yan daba a Unguwar Oke-Agodi Alfa Yahaya da ke Ilorin sun kai hari kan jami’an hukumar kashe gobara ta Jihar Kwara tare da raunata wasu jami’an kashe gobara guda biyu a gidan man K&R Petroleum Nigeria Limited.

“Daya daga cikin tawagar sojojin Nijeriya da suka zo kwantar da tarzoma su ma sun yi ta harbin kan mai uwa da wabi, hasali ma dai wannan sojan ya samu rauni.

“Saboda haka, daraktan hukumar kashe gobara ta Jihar Kwara, Prince Falade John Olumuyiwa, ya bayyana alhininsa game da faruwar lamarin tare da bayyana al’ummar yankin Agodi a matsayin masu nuna rashin godiya da rashin yaba wa kokarin ‘yan kwana-kwana.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan DabaKwaraSoja
ShareTweetSendShare
Previous Post

PDP Ta Fito Da Sabon Salon Yakin Neman Zabe A Sakkwato

Next Post

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Isa Birnin Riyadh Kasar Saudiyya

Related

Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci

4 hours ago
Sojoji
Manyan Labarai

DHQ Za Ta Tura Dakaru Na Musamman 800 Yankunan Da Ke Fama Da Rashin Tsaro – CDS

9 hours ago
Gwamnatin APC Ta Kara Ingiza ‘Yan NIjeriya Cikin Bakin Talauci – PDP
Manyan Labarai

PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta

12 hours ago
KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano
Manyan Labarai

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

16 hours ago
Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano
Manyan Labarai

Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

19 hours ago
Sabbin Ministoci
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6

1 day ago
Next Post
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Isa Birnin Riyadh Kasar Saudiyya

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Isa Birnin Riyadh Kasar Saudiyya

LABARAI MASU NASABA

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

June 25, 2025
Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

June 25, 2025
Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

June 25, 2025
MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

June 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci

June 25, 2025
Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato

Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato

June 25, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa

Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa

June 25, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Katse Hanyar Maiduguri Zuwa Damboa

Mutane 4 Sun Mutu, 10 Sun Jikkata Yayin Da Wata Mota Ta Taka Bam A Borno

June 25, 2025
Shawarar Gudanar Da Harkokin AI Na Duniya Na Jagorantar Ci Gaban Wayewar Kan Dan Adam Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani

Shawarar Gudanar Da Harkokin AI Na Duniya Na Jagorantar Ci Gaban Wayewar Kan Dan Adam Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani

June 25, 2025
Sojoji

DHQ Za Ta Tura Dakaru Na Musamman 800 Yankunan Da Ke Fama Da Rashin Tsaro – CDS

June 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.