• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Kasuwar Afrika Sun Gano Zarafi Mai Kyau A Canton Fair

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
‘Yan Kasuwar Afrika Sun Gano Zarafi Mai Kyau A Canton Fair
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Ana gudanar da bikin baje kolin kayayyakin shige da fice na kasar Sin wato Canton Fair a birnin Guangzhou dake kudancin kasar Sin. A yayin bikin baje kolin, na bi wani dan kasuwa daga Najeriya Dawud Jidda Jidda don fahimtar yadda zai gudanar da aikin sayayya a wannan biki. Dawud ya kai ni wani shago mai samar da allunan tattara hasken rana don samar da wutar lantarki, inda ya ce: “Allunan da kamfanonin Sin suka samar na da inganci matuka, kuma ‘yan kasuwar Najeriya na matukar sonsu. Ban da hajoji masu amfani da makamashi mai tsabta, suna kuma gamsuwa da kayayyakin lanturoni da Sin ta samar. Na shafe tsawon shekaru 3 a nan kasar Sin, kuma na halarci bikin baje kolin Canton Fair sau 3. A wannan karo, abokaina daga Najeriya sun ba ni odar sayen hajoji daga kasar Sin, kuma wannan biki ya zama dandali mafi kyau wajen zabar hajojin.”

Ban da wannan kuma, Dawud ya gaya min cewa, ya zabi kamfanoni 3 masu inganci, kuma abu na gaba shi ne, tattauna farashi.

  • Hungary Na Sa Ran Ziyarar Xi Za Ta Bude Sabon Babi A Dangantakarta Da Sin
  • Shugaban Serbia: Zan Rubuta Wani Littafi Don Tunawa Da Hulda Ta Da Xi Jinping

A yini na biyu, ya kai ni dakin ajiye hajoji wanda ya kafa bisa hadin gwiwa da ‘yan kasuwa Sinawa, inda ake kokarin kunshe hajoji da sanya su cikin akwatunan da za a yi jigilarsu ciki, kana ana gudanar da ayyuka bisa tsari mai kyau. Ya kara da cewa, ana jigilar hajoji ta jirgin ruwa a kalla sau 2 ko 3 a ko wane mako, kuma ana iya tattara mabambanta hajoji cikin akwati daya. Har ila yau, ya ce a baya, jigilar kayayyaki zuwa Nijeriya kan dauki watanni 6, amma yanzu hajoji suna isa tashar jirgin ruwa a Najeriya, cikin watanni 2 ko 3.

Kazalika, Dawud ya ce, yana zabar nagartattun hajoji a Canton Fair, da gudanar da cinikayya ta hanyar hadin gwiwa da Sinawa abokansa, kuma gwamnatin Sin ta samar da manufofin kwastam masu kyau. Ya ce bunkasuwar Sin na ba shi zarafi mai kyau wajen gudanar da harkokin cinikayya, inda ya bayyana birnin Guangzhou a matsayin mafarin ciniki, kana mafarin zaman rayuwa mai inganci. (Mai Zane da rubutu: MINA)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaJapanSinUkraine
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ranar Ma’aikata: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranar Laraba A Matsayin Hutu

Next Post

‘Yar Sanda Da Wata Sun Shiga Hannu Kan Sato Yara 5 Daga Sakkwato

Related

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

16 hours ago
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

17 hours ago
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12
Daga Birnin Sin

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

18 hours ago
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana
Daga Birnin Sin

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

19 hours ago
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

20 hours ago
Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa
Daga Birnin Sin

Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

21 hours ago
Next Post
Uba Ya Hallaka Dansa Daya Tilo Kan Cacar-baki

'Yar Sanda Da Wata Sun Shiga Hannu Kan Sato Yara 5 Daga Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

August 23, 2025
2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

August 23, 2025
Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.