• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Miliyan 1.8 Ne Ke Fama Da Matsalar Yunwa – Hukumar FAO

by Sulaiman and Abubakar Abba
7 months ago
in Noma Da Kiwo
0
‘Yan Nijeriya Miliyan 1.8 Ne Ke Fama Da Matsalar Yunwa – Hukumar FAO
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar samar da abinci da kula da aikin noma ta duniya (FAO), ta sanar da cewa; a halin yanzu ‘yan Nijeriya miliyan 1.8 ne ke fama da matsalar yunwa.

Karamin Ministan Ma’aikatar Noma da Samar da Wadataccen Abinci, Aliyu Sabi Abdullahi; ya sanar da hakan ne a Abuja, wajen taron manema labarai.

  • MDD Za Ta Yi Duk Mai Yiwuwa Wajen Taimaka Wa Nijeriya Kawo Karshen Talauci
  • Kamfanoni 80 Sun Bayyana Burinsu Na Halartar Baje Kolin CIIE Karo Na 8

Sai dai, Abdullahi ya shelanta cewa; gwamnatin tarayya ta mayar da hankali wajen yakar rashin abinci a kasar, inda ya yi nuni da cewa; a 2023, mutane miliyan 733 ne ke fuskantar yunwa a dukkanin fadin duniya.

Ministan, wanda ya bayyana haka a bikin ranar abinci ta duniya da aka gudanar a kwanakin baya ya ci gaba da cewa, bisa rahoton yanzu da hukumar FAO ta wallafa kan karancin abinci da kuma abinci mara gina jiki da mutane ke fuskanta ya kai miliyan 733 a 2023 a fadin duniya.

Ya kara da cewa, kimanin mutane biliyan 2.33 sun fuskanci karancin abinci a 2023, inda kuma mutane biliyan 2.8 a 2022, ba sa iya samun abinci mai gina jiki.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

Ya yi gargadin cewa, idan har mahukunta a kasar ba su dauki matakan da suka kamata ba, kimanin ‘yan Nijeriya miliyan 582 ne za su fuskanci rashin samun abinci mai gina jiki nan da 2030.

Abdullahi ya sanar da cewa, akwai manyan kalubale da dama da suka haifar da karancin abinci a duniya da suka hada da sauyin yanayi, fari, yawan samun ruwan sama da sauransu.

A cewar tasa, wadannan kalubalen sun kasance barazana a kan harkokin noma baki-daya, sannan kuma ya danganta da karancin abincin da ake ci gaba da samu a kasar sakamakon rashin tsaro, matsin tattalin arziki, annobar ambaliyar ruwan sama da kuma cire tallafin mai.

Sai dai, ya sanar da cewa; don mangance wadannan kalubale, wadanda kuma suka zamo karfen kafa wajen cimma burin da gwamnatin tarayya ta sanya a gaba na samar da wadataccen abinci a kasar, gwamnatin ta wanzar da sauye-sauye da dama da suka hada da kirkiro da ayyukan yi da kuma rage tsadar kayan abinci.

Ya kara da cewa, dole ne har sai masu ruwa da tsaki a wannan kasa, su ma sun bayar da tasu gudunmawar; kafin a iya kawo karshen wadannan matsaloli.

A cewarsa, a shekarar 2017; Nijeriya ta samu gagarumar nasara a fannin aikin noma a duniya, inda ta kai mataki na daya a fannin noman Rogo da Doya, inda ta noma wadannan amfani da suka kai kimanin tan miliyan 59.4 da kuma tan miliyan 47.9 baki-daya.

Bugu da kari, ya kara da cewa; Nijeriya ta kai mataki na 14 wajen noman Masara, inda ta noma tan miliyan 10.42; ta kai mataki na hudu a fannin noman Kwakwar manja, inda ta noma tan miliyan 7.7 a cikin shekara guda.
Kazalika a 2019, Nijeriya ce kan gaba wajen noman Shinkafa a dukkanin Nahiyar Afirka, inda aka noma tan miliyan tara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kangin TalauciYunwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kingibe Ya Yaba Wa Tsare-tsaren Bunkasa Ilimi Ga Matasa Na Buratai

Next Post

Gwamnatin Tarayya Da EU Sun Kulla Yarjejeniyar Bunkasa Wutar Lantarki

Related

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

3 hours ago
Neja
Noma Da Kiwo

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

10 hours ago
Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

1 week ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

2 weeks ago
Next Post
Discos

Gwamnatin Tarayya Da EU Sun Kulla Yarjejeniyar Bunkasa Wutar Lantarki

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
FAO

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.