• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Miliyan 1.8 Ne Ke Fama Da Matsalar Yunwa – Hukumar FAO

by Sulaiman and Abubakar Abba
10 months ago
in Noma Da Kiwo
0
‘Yan Nijeriya Miliyan 1.8 Ne Ke Fama Da Matsalar Yunwa – Hukumar FAO
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar samar da abinci da kula da aikin noma ta duniya (FAO), ta sanar da cewa; a halin yanzu ‘yan Nijeriya miliyan 1.8 ne ke fama da matsalar yunwa.

Karamin Ministan Ma’aikatar Noma da Samar da Wadataccen Abinci, Aliyu Sabi Abdullahi; ya sanar da hakan ne a Abuja, wajen taron manema labarai.

  • MDD Za Ta Yi Duk Mai Yiwuwa Wajen Taimaka Wa Nijeriya Kawo Karshen Talauci
  • Kamfanoni 80 Sun Bayyana Burinsu Na Halartar Baje Kolin CIIE Karo Na 8

Sai dai, Abdullahi ya shelanta cewa; gwamnatin tarayya ta mayar da hankali wajen yakar rashin abinci a kasar, inda ya yi nuni da cewa; a 2023, mutane miliyan 733 ne ke fuskantar yunwa a dukkanin fadin duniya.

Ministan, wanda ya bayyana haka a bikin ranar abinci ta duniya da aka gudanar a kwanakin baya ya ci gaba da cewa, bisa rahoton yanzu da hukumar FAO ta wallafa kan karancin abinci da kuma abinci mara gina jiki da mutane ke fuskanta ya kai miliyan 733 a 2023 a fadin duniya.

Ya kara da cewa, kimanin mutane biliyan 2.33 sun fuskanci karancin abinci a 2023, inda kuma mutane biliyan 2.8 a 2022, ba sa iya samun abinci mai gina jiki.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Ya yi gargadin cewa, idan har mahukunta a kasar ba su dauki matakan da suka kamata ba, kimanin ‘yan Nijeriya miliyan 582 ne za su fuskanci rashin samun abinci mai gina jiki nan da 2030.

Abdullahi ya sanar da cewa, akwai manyan kalubale da dama da suka haifar da karancin abinci a duniya da suka hada da sauyin yanayi, fari, yawan samun ruwan sama da sauransu.

A cewar tasa, wadannan kalubalen sun kasance barazana a kan harkokin noma baki-daya, sannan kuma ya danganta da karancin abincin da ake ci gaba da samu a kasar sakamakon rashin tsaro, matsin tattalin arziki, annobar ambaliyar ruwan sama da kuma cire tallafin mai.

Sai dai, ya sanar da cewa; don mangance wadannan kalubale, wadanda kuma suka zamo karfen kafa wajen cimma burin da gwamnatin tarayya ta sanya a gaba na samar da wadataccen abinci a kasar, gwamnatin ta wanzar da sauye-sauye da dama da suka hada da kirkiro da ayyukan yi da kuma rage tsadar kayan abinci.

Ya kara da cewa, dole ne har sai masu ruwa da tsaki a wannan kasa, su ma sun bayar da tasu gudunmawar; kafin a iya kawo karshen wadannan matsaloli.

A cewarsa, a shekarar 2017; Nijeriya ta samu gagarumar nasara a fannin aikin noma a duniya, inda ta kai mataki na daya a fannin noman Rogo da Doya, inda ta noma wadannan amfani da suka kai kimanin tan miliyan 59.4 da kuma tan miliyan 47.9 baki-daya.

Bugu da kari, ya kara da cewa; Nijeriya ta kai mataki na 14 wajen noman Masara, inda ta noma tan miliyan 10.42; ta kai mataki na hudu a fannin noman Kwakwar manja, inda ta noma tan miliyan 7.7 a cikin shekara guda.
Kazalika a 2019, Nijeriya ce kan gaba wajen noman Shinkafa a dukkanin Nahiyar Afirka, inda aka noma tan miliyan tara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kangin TalauciYunwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kingibe Ya Yaba Wa Tsare-tsaren Bunkasa Ilimi Ga Matasa Na Buratai

Next Post

Gwamnatin Tarayya Da EU Sun Kulla Yarjejeniyar Bunkasa Wutar Lantarki

Related

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

4 days ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

4 days ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

2 weeks ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

2 weeks ago
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

2 weeks ago
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya
Noma Da Kiwo

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

3 weeks ago
Next Post
Discos

Gwamnatin Tarayya Da EU Sun Kulla Yarjejeniyar Bunkasa Wutar Lantarki

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

August 27, 2025
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.