• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan sanda Sun Kaddamar Da Cibiyar Yin Rijistar Motoci Ta Na’urar Zamani A Kebbi

by Umar Faruk
1 year ago
in Labarai
0
‘Yan sanda Sun Kaddamar Da Cibiyar Yin Rijistar Motoci Ta Na’urar Zamani A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘Yan sandan Jihar Kebbi ta kaddamar da ofishin rajistar motoci ta na’urar zamani (CMR) domin yaki da masu aikata miyagun laifukan satar abin hawa.

Bukatar yin rajistar motocin na kunshe ne a cikin wata takardar manema labarai mai dauke da sa hannun kakakin rundunar ‘Yan sandan Jihar Kebbi, SP Nafi’u Abubakar, inda aka raba wa manema labarai a Birnin Kebbi.

  • Farashin Kayan Abinci Ya Ƙaru A Jihohin Nijeriya 36, Abuja, Kano, Borno Farashin Kaya Ya Sauka
  • Gidauniyar M-TECH Ta Tallafawa Yara Mabukata 400 Da Tallafin Karatu A Jihar Kebbi

Kazalika takardar ta kara da cewa, “A bisa shirin babban sufeton ‘Yan sanda na 22, IGP Kayode Adeolu Egbetokun, NPM, Ph.D, na inganta harkokin tsaro a cikin gida Nijeriya, rundunar ‘yansandan jihar Kebbi ta bayar da umarnin kaddamar da babban ofishin yin rigistar motocin ta na’urar zamani wato ‘Digitalized Central Motor vehicle Registry (CMR)’ da ke Hedikwatar Rundunar a Gwadangaji, da ke a Birnin Kebbi.

Haka kuma ta kara ta cewa an yi shi ne don magance laifukan da suka shafi abubuwan hawa da nufin inganta lafiyar jama’a da tsaron mutanen jihar Kebbi.

Takardar ta ci gaba da cewa, duba da yadda manyan laifukan da suka shafi motoci ke karuwa, rundunar ‘yan sandan Nijeriya ta sake farfado da babban ofishin rajistar motoci ta hanyar sanya shi a cikin na’ura mai kwakwalwa ta yadda za a rika amfani da bayanan mota guda domin ya ba da hakikanin bayanai daga ’yansandan a yayin gudanar da bincike na zamani wajen kokawa da laifukan satar motoci a fadin jahohin kasar nan.

Labarai Masu Nasaba

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har ilayau, kaddamar da ofishin rajista yana da fa’idodi masu yawa, waɗanda suka haɗa da; inganta tsaro da samun bayanai na kai-tsaye daga na’urar CMR ga ‘yan ƙasa, haka kuma za su iya samun babban kwarin gwiwa ga tsaron motocinsu.

Haka kuma ingantattun bayanan abin hawa za su taimaka wajen dakile wa da magance laifuka satar motoci cikin sauki, da nufin tabbatar da cewa, an kiyaye kadarorin ‘yan kasa.

Hakazalika, ‘Yan sandan za su kasance mafi kyawun kayan aiki don aiwatar da dokokin da suka shafi motoci, kamar rajista da lasisi. Hakan zai haifar da samar da ingantattun hanyoyi da inganta hanyoyin tafiyar da ababen hawa da za su amfanar da duk masu amfani da ababen hawansu a kan hanya.

Bugu da kari takardar ta ce cikakkun bayanai na motoci za su zama abin hana masu aikata laifuka waɗanda za su iya amfani da ababen hawa don ayyukan da ba su dace ba. Sanin cewa jami’an tsaro na da damar samun ingantattun bayanai na iya hana aikata laifukan satar motoci a jahohin kasar nan.

Don haka Kwamishinan ’Yan sandan Jihar Kebbi, CP Chris Aimionowane, psc, mnips, ya bukaci al’ummar Jihar masu son zaman lafiya da su rungumi shirin na IGP na kawo sauyi ta hanyar yiwa motocinsu rajistar ta na’uran zamani da nufin bayar da gudunmawarsu tare da inganta tsaro na cikin gida da tabbatar da tsaro ga kowa da kowa.

Daga karshe don yin rijistar motar ku, ku ziyarci https://cmris.npf.gov.ng ko tuntuɓi Jami’in da ke kula da ofishin yin rigiata a rundunar ‘yansanda ta jihar akan wannan Lamba 08062118443 ko don neman karin bayani.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan SandaKebbiMotociTsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

2024 Hajj: Karancin Maniyyata Ba Nijeriya Kadai Ya Shafa Ba – NAHCON

Next Post

Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Related

Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

14 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

14 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

15 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

16 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

18 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

19 hours ago
Next Post
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.