ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Takaran Gwamna 8 Sun Mara Wa Gwamnan Gombe Baya

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Gombe

‘Yan takaran gwamnan Jihar Gombe su takwas daga jam’iyyun adawa daban-daban sun mara tazarcen gwamnan Jihar, Muhammadu Inuwa Yahaya baya, tare da yin alkawarin taya shi aiki don samun nasara a zaben gwamnoni da ‘yan majalisun jihohi da ke tafe ranar Asabar.

Shugaban gamayyar tuntuba tsakanin jam’iyyun siyasa na jihar (IPAC) kuma dan takaran gwamna na Jam’iyyar Zenith Labour Party, Muhammad Gana Aliyu shi ne ya bayyana hakan yayin wata zantawa da manema labarai a ofishin sa dake Gombe.

  • Dan Bindiga Ya Shiga Hannu, Ya Bayyana Yadda Ya Kashe Mutum 15 A Katsina
  • Kotu Ta Daure Tsohon Kwamishina Shekara 3 Kan Almundahanar Miliyan 180 A Imo

Ya ce, sun dauki matakin ne bayan doguwar tattaunawa da nazari kan nasarorin da gwamnati mai ci ta samu a karkashin jagorancin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Mun cimma wannar muhimmiyar matsaya ce bayan da muka yi nazari sosai kan yadda Gwamna Inuwa yake gudanar da ayyukan sa musamman ta fuskar samar da zaman lafiya, da tsaro da ilimi, da kiwon lafiya, da samar da ababen more rayuwa da ayyukan jinlai a faɗin jihar”.

Shugaban na IPAC ya ce, ‘yan takaran da suka mara baya ga gwamnan na Gombe kuma dan takaran gwamna na Jam’iyyar APC su ne: Muhammad Gana Aliyu na Jam’iyyar Zenith Labour Party (ZLP), da Sulaiman Abubakar Sunusi na Jam’iyyar National Rescue Movement (NRM), da Sadiq Abdulhamid na Jam’iyyar Boot Party (BP) da Adamu Muhammad na Jam’iyyar Action Peoples Party (APP).

LABARAI MASU NASABA

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Sauran sun hada da Sulaiman Jibrin na Jam’iyyar Action Democratic Party (ADP), da Adamu Aliyu Ɗanmakka na Jam’iyyar African Action Congress (AAC), sai Kelmi Jacob Lazarus na Jam’iyyar Social Democratic Party (SDP) da Muhammad Bello Abubakar na Jam’iyyar Allied Peoples Party (APP).

‘Yan takaran sun kuma yi kira ga magoya bayan su dasu zabi Gwamna Inuwa Yahaya don ba shi damar dorawa kan yunkurin sa na samar da ayyukan ci gaba mai ɗorewa a jihar.

‘Yan takaran gwamnan takwas da suka amincewa Gwamna Inuwa suna daga cikin ‘yan takara 13 da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya wadda Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta kasa (INEC) da hadin gwiwar Kwamitin Tuntuba Tsakanin Hukumomi Kan Harkokin Tsaro (ICCES) suka shirya a ranar 15 ga watan Fabrairun wannar shekara.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwankwaso
Labarai

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?
Nazari

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
Next Post
Zaben Gwamnoni: INEC Ta Gargadi Jam’iyyun Siyasa Kan Tada Tarzoma

Zaben Gwamnoni: INEC Ta Gargadi Jam'iyyun Siyasa Kan Tada Tarzoma

LABARAI MASU NASABA

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025
Kwankwaso

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025
Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

November 15, 2025
Za A Yi Gwanjon Rigunan Messi Na Gasar Kofin Duniya Ta 2022 Da Kudi Tsagwagwa

Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi

November 15, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

November 15, 2025
Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

November 15, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.