ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Wasa Biyar Da Tauraruwarsu Za Ta Haska A AFCON

by Abba Ibrahim Wada
15 hours ago
AFCON

Kamar yadda hukumar kwallon kafa ta nahiyar Afirka CAF ta shirya, za a fara gasar cin kofin kwallon kafa ta nahiyar Afirka karo na 35 a kasar Moroko a ranar 21 ga watan Disamban 2025, kuma za a buga wasan karshe ne ranar 18 ga watan Janairun 2026.

Mai masaukin za ta so ta dauki kofin karo na farko tun 1976, yayin da shi kuma Mohammed Salah zai so manta da abin da ke faruwa a Liberpool ta hanyar taimaka wa kasarsa Masar ta lashe kofin tun bayan hakan da ta yi a 2010.

  • An Bukaci Amurka Da Ta Kauracewa Sanya Wasu Sassa Na Muzgunawa Kasar Sin Cikin Kudurin Dokar Tsaron Kasa
  • Yawan Jarin Waje Da Kasar Sin Ta Yi Amfani Da Shi A Watan Nuwamban Bana Ya Karu Da Kaso 26.1%

Akwai zakakuran ‘yan wasa da dama da tauraruwarsu za ta haskaka a gasar ta bana wadda manyan ‘yan wasan Afirka daga manyan kasashe daban-daban za su fafata domin samun zakaran wannan shekarar.

ADVERTISEMENT

Azzedine Ounahi (Moroko)

Dan wasan Real Madrid dan asalin Moroko Brahim Diaz shi ne ya fi jefa kwallaye a wasan neman gurbi, to amma Azzesina Ounahi, wanda shi ne ke kokari wajen raba kwallo a tsakiyar tawagar Moroko shi ne dan wasan da ‘yan Moroko za su so su ga yana taka rawar gani a gasar da za a buga a gaban dubban ‘yan kasar.

LABARAI MASU NASABA

FIFA Za Ta Bayar Da Dala Miliyan 50 Ga Kasar Da Ta Lashe Gasar Cin Kofin Duniya

Da Ɗumi ɗumi: Mafarkin Nijeriya Na Zuwa Gasar Kofin Duniya Na Dab Da Cika

Matashin wanda ya samu horo a shahararriyar cibiyar horas da ‘yan wasa ta Sarki Mohammed BI, Ounahi ya daure zaman takaici a kungiyar Marseille bayan tafiya kungiyar sanadiyyar rawar gani da ya taka a gasar kofin duniya ta 2022.

Sai dai bayan komawarsa zuwa kungiyar Girona a Sifaniya cikin watan Agusta, tauraruwarsa ta dawo tana haskawa. Moroko, wadda za ta kara da kasashen Comoros da Mali da kuma Zambia a rukunin (A), suna kuma da kwararrun ‘yan wasa kamar mai tsaron raga Yassine Bonou da dan wasan gaba Youssed En-Nesyri.

Mohamed Amoura (Algeria)MAGES

Dan wasan gaban na Wolfsburg ya jefa kwallo 11 wa kasarsa cikin wasanni takwas tun daga watan Maris, ciki har da kwallo uku rigis da ya zura a ragar Mozambikue. Kuma

wannan bajinta da ya nuna ta sa ya zama zabi na farko a tawagar kasarsa.

Duk da cewa Riyad Mahrez ne ginshiki a tawagar, to amma Amoura ya gina kansa a cikin tawagar. Dole ne kasashen Sudan da Butkina Faso da kuma Ekuatorial Guinea da suke tare a rukunin (E) su yi taka-tsantsan da shi saboda yadda yake sharafi a wannan lokacin.

Bictor Osimhem (Nijeriya)

Kawo yanzu za a iya cewa nasarar Nijeriya kusan za a ce ta ta’allaka ne ga rawar da wannan matashin da ke wasa a kungiyar Galatasaray ke takawa a wannan lokacin musamman yadda yake zura kwallaye a kowanne lokaci.

Tawagar Super Eagles ta Nijeriya ta samu maki 4 ne kacal a cikin 15 da za ta iya samu lokacin da dan wasan mai shekara 26 ba ya nan, a wasannin neman gurbin zuwa gasar cin kofin duniya.

Osimehn na cikin ginshikan kungiyar a karkashin mai horaswa Eric Chelle, kuma Nijeriya ta kasa lashe wasanta na neman cike gurbi da DR Congo, lokacin da aka cire shi a hutun rabin lokaci.

Kokarin da Osimhen zai yi a zai taimaka matukar gaske idan har Nijeriya na son ta matsa gaba daga matsayi na biyu da ta samu a gasar da aka buga a Ibory Coast zuwa lashe gasar gaba daya. Nijeriya, wadda ta lashe kofin sau uku ta fito a cikin rukunin da ya hada da kasashen Tanzania da Uganda da kuma Tunisia a rukunin (C).

Ibrahim Mbaye (Senegal)

Kowa ya san Sadio Mane ne ginshikin kasar a gasar AFCON ta 2021, yayin da Iliman Ndiaye da Ismaila Sarr suke taka rawar gani a gasar Premier, lamarin da ya sa aka samu ‘yan wasan gaba uku gogaggu.

Tsohon dan wasan tawagar matasa ta kasar Faransa, ya samu shiga tawagar manya ta kungiyar PSG a wannan kaka, inda ya fara a wasan da kungiyarsa ta doke Barcelona a farkon kaka.

Mbaye ya fara buga wa Senegal wasa ne a watan da ya gabata a karawarsu da Brazil, sannan ‘yan kwanaki bayan ya zama dan wasa mafi karancin shekaru a kungiyarsa,inda yana da shekra 17.

 

Rogers Mato (Uganda)

Tawagar ‘yanwasan Uganda ta dawo AFCON tun daga shekara 2019 lokacin da aka fitar da ita a zagayen ‘yan 16, yanzu kuma suna hankoron kai wa wasan karshe a wannan gasa. Kungiyar da ke karkashin jagorancin Paul Put ta kammala a mataki na biyu a rukuninsu na wasannin neman gurbin gasar cin kofin duniya, a bayan Algeria.

Uganda za ta fuskanci jarrabawa a rukunin (C) inda za ta kara da kasashe kamar Nijeriya da Tunisia.

Reinildo (Mozambikue)

Mozambikue za ta isa Moroko a matsayin kasar da ba ta taba zuwa zagayen kifa daya kwala ba a karo biyar da ta halarci gasar AFCON. Sai dai a karon farko tana alfahari da kasancewar daya daga cikin ‘yan wasan gasar Premier a tawagarsu, bayan da Reinildo ya zamo dan kasar Mozambikue na farko da ya buga wasa a gasar Premier bayan ya koma kungiyar Sunderland daga Atletico Madrid a watan Yuli. Wanda ke wasa ta bangaren hagu, dan wasan mai shekara 31 ya taimaka wa kungiyarsa wajen yin ba-zata

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

FIFA Za Ta Bayar Da Dala Miliyan 50 Ga Kasar Da Ta Lashe Gasar Cin Kofin Duniya
Wasanni

FIFA Za Ta Bayar Da Dala Miliyan 50 Ga Kasar Da Ta Lashe Gasar Cin Kofin Duniya

December 17, 2025
Da Ɗumi ɗumi: Mafarkin Nijeriya Na Zuwa Gasar Kofin Duniya Na Dab Da Cika
Manyan Labarai

Da Ɗumi ɗumi: Mafarkin Nijeriya Na Zuwa Gasar Kofin Duniya Na Dab Da Cika

December 16, 2025
AFCON 2026: ‘Yan Wasa 10 Da Suka Isa Sansanin Super Eagles Zuwa Yanzu
Wasanni

AFCON 2026: ‘Yan Wasa 10 Da Suka Isa Sansanin Super Eagles Zuwa Yanzu

December 15, 2025
Next Post
HOTUNA: Yadda Tinubu Ya Kai Ziyara Don Ta’aziyyar Sheikh Dahiru Bauchi

HOTUNA: Yadda Tinubu Ya Kai Ziyara Don Ta'aziyyar Sheikh Dahiru Bauchi

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025
An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

December 20, 2025
Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

December 20, 2025
An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin

An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin

December 20, 2025
Shugaban Somaliya: Kara Fadada Bude Kofa Ga Kasashen Waje Da Sin Ke Yi Zai Inganta Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka

Shugaban Somaliya: Kara Fadada Bude Kofa Ga Kasashen Waje Da Sin Ke Yi Zai Inganta Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.