‘Yan wasa akalla 10 ne suka isa sansanin Super Eagles yayin da ake fara shirye-shiryen gasar cin kofin kasashen Afirka ta 2025 (AFCON), an bude sansanin Super Eagles a hukumance a ranar Lahadi a Renaissance Hotels dake birnin Alkahira, tare da dukkan masu horarwa da ma’aikatan da ke aiki a ciki da wajen gasar.
Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) ya ruwaito cewa mai tsaron gida Francis Uzoho shi ne dan wasa na farko da ya isa, inda ya sauka da misalin karfe 2 na rana agogon Nijeriya, an zabi Uzoho a matsayin daya daga cikin masu tsaron raga uku dake cikin tawagar Super Eagles Mai dauke da yan wasa 28 da kocin Eric Chelle ya gayyata, wanda hakan ya nuna komawarsa cikin tawagar bayan shafe fiye da shekara daya yana jinya.
Stanley Nwabali ne ya zo na biyu a cikin wadanda suka fara halartar sansanina, yayin da Fisayo Dele-Bashiru da Ebenezer Akinsanmiro suka Isa sansanin daga baya wanda ya kara yawan yan wasan zuwa hudu, sauran yan wasa shida da suka isa daga baya sun hada da Amas Obasogie, Semi Ajayi, Ademola Lookman, Igho Ogbu, Bright Osayi-Samuel da Tochukwu Nnadi, wanda hakan ya kawo jimillar yan wasa a sansanin zuwa goma.
Ana sa ran karin yan wasa za su shiga cikin sa’o’i masu zuwa yayin da Nijeriya ke kara shiri don gasar cin kofin nahiyar, NAN ta kuma ruwaito cewa zakarun na Afirka sau uku za su yi atisaye na farko a maraicen yau, a wani bangare na shirye-shiryensu, Super Eagles za ta buga wasan sada zumunta da Pharaohs of Egypt a ranar Talata a filin wasa na kasa da kasa dake birnin Cairo.














