ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki

by Sani Anwar and Sulaiman
5 months ago
Yajin aiki

Kungiyar Ma’aikatan Kananan Hukumomin Nijeriya (NULGE), ta koka kan ci gaba da jinkirin aiwatar da hukuncin da kotun koli ta yanke na bai wa kananan hukumomi ‘yancin cin gashin kansu.

Babban lauyan gwamnatin tarayya (AGF), kuma ministan shari’a, Lateef Fagbemi ne a madadin gwamnatin tarayya; ya kai karar jihohin kasar nan 36, kan yadda gwamnonin ke tafiyar da kudaden kananan hukumomi.

  • Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
  • NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

A cikin karar, mai lamba SC/CB/343/2024; babban lauyan gwamnatin tarayyar (AGF), ya kuma roki kotun da ta bayar da umarnin haramta wa gwamnonin jihohi rusa shugabannin kananan hukumomi, ba bisa ka’ida ba.

ADVERTISEMENT

LEADERSHIP ta rawaito cewa, kukan da gwamnonin jihohi suka yi a kan kudaden kananan hukumomi ta hanyar asusun hadin gwiwa a tsakaninsu (Jihohi da kananan hukumomi), ya dakile wannan mataki na gwamnati tare da takaita ci gaban kasa a fadin kasar.

Sai dai, shekara guda cif da kotun koli ta yanke hukuncin da ya tabbatar da cikakken ikon cin gashin kai ga kananan hukumomi 774 a Nijeriya, har yanzu ba a aiwatar da shi ba a dukkanin fadin jihohin wannan kasa, kungiyar ta NULGE ta bayyana hakan a matsayin cin zarafi da gangan ga ci gaban wannan kasa.

LABARAI MASU NASABA

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

A tattaunawarsa da da LEADERSHIP, Shugaban Kungiyar NULGE na Kasa, Aliyu Haruna Kankara, ya zargi gwamnonin jihohi da shirya wani shiri da gangan na yi wa shari’a zagon kasa, wanda hakan ke kawo cikas ga ci gaban kasa da kuma jin dadin ma’aikatan kananan hukumomi.

Kankara, ya kuma yi gargadin cewa; kungiyar za ta iya shiga yajin aiki a dukkanin fadin kasar, idan har gwamnatin tarayya ta gaza aiwatar da hukuncin da ya dace.

Kankara ya danganta jinkirin da aka samu wajen aiwatar da ‘yancin cin gashin kan, ta bangaren harkokin kudi da dabarun siyasa da gwamnatocin jihohin ke yi.

Har ila yau, ya yi zargin cewa; gwamnonin sun jajirce wajen nuna adawarsu ga ‘yancin cin gashin kan kananan hukumomin tare da kawo cikas ga samun kudadensu, duk da hukuncin da kotun kolin ta yanke a 2024.

“Babu wani abu da zai hana aiwatar da wannan hukunci, sai gwamnonin da suka yi wa ‘yan Nijeriya damfara ta hanyar yin awon gaba da kudaden kananan hukumomi. Ba wata tangardar doka ba ce, illa kawai dai tsantsar adawa ta siyasa, kamar yadda shugaban ya bayyana wa LEADERSHIP.

Kotun koli ta yanke shari’a a shekarar da ta gabata tare da bayar da umarnin a biya kudaden da ake ware wa kananan hukumomi kai tsaye a cikin asusunsu, domin kauce wa katsalandan din gwamnatin jihohi. Sai dai, bayan shekara guda cif da yanke hukuncin, Kankara ya koka da yadda ba a aiwatar da hukuncin ba, musamman saboda rashin kishi daga hukumomin jihohi da na kuma tarayya.

Wannan dalili ne a cewar tasa, ya jefa kananan hukumomi cikin mawuyacin hali da kuma kunci.

Cikin takaicin jinkirin da ake yi, shugaban NULGE ya bayyana cewa; kungiyar za ta kara kaimi wajen ganin an aiwatar da hukuncin kotun kolin.

Kankara ya bayyana cewa, kungiyar za ta ci gaba da yin fafutuka tare da kulla alaka mai karfi da kungiyoyi masu zaman kansu da hukumomin kasa da kasa da kuma kungiyar kwadago ta Nijeriya (NLC), domin matsa wa gwamnatin tarayya lamba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa
Labarai

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli
Labarai

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba

Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.