• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki

by Sani Anwar and Sulaiman
3 months ago
Yajin aiki

Kungiyar Ma’aikatan Kananan Hukumomin Nijeriya (NULGE), ta koka kan ci gaba da jinkirin aiwatar da hukuncin da kotun koli ta yanke na bai wa kananan hukumomi ‘yancin cin gashin kansu.

Babban lauyan gwamnatin tarayya (AGF), kuma ministan shari’a, Lateef Fagbemi ne a madadin gwamnatin tarayya; ya kai karar jihohin kasar nan 36, kan yadda gwamnonin ke tafiyar da kudaden kananan hukumomi.

  • Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
  • NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

A cikin karar, mai lamba SC/CB/343/2024; babban lauyan gwamnatin tarayyar (AGF), ya kuma roki kotun da ta bayar da umarnin haramta wa gwamnonin jihohi rusa shugabannin kananan hukumomi, ba bisa ka’ida ba.

LEADERSHIP ta rawaito cewa, kukan da gwamnonin jihohi suka yi a kan kudaden kananan hukumomi ta hanyar asusun hadin gwiwa a tsakaninsu (Jihohi da kananan hukumomi), ya dakile wannan mataki na gwamnati tare da takaita ci gaban kasa a fadin kasar.

Sai dai, shekara guda cif da kotun koli ta yanke hukuncin da ya tabbatar da cikakken ikon cin gashin kai ga kananan hukumomi 774 a Nijeriya, har yanzu ba a aiwatar da shi ba a dukkanin fadin jihohin wannan kasa, kungiyar ta NULGE ta bayyana hakan a matsayin cin zarafi da gangan ga ci gaban wannan kasa.

LABARAI MASU NASABA

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

A tattaunawarsa da da LEADERSHIP, Shugaban Kungiyar NULGE na Kasa, Aliyu Haruna Kankara, ya zargi gwamnonin jihohi da shirya wani shiri da gangan na yi wa shari’a zagon kasa, wanda hakan ke kawo cikas ga ci gaban kasa da kuma jin dadin ma’aikatan kananan hukumomi.

Kankara, ya kuma yi gargadin cewa; kungiyar za ta iya shiga yajin aiki a dukkanin fadin kasar, idan har gwamnatin tarayya ta gaza aiwatar da hukuncin da ya dace.

Kankara ya danganta jinkirin da aka samu wajen aiwatar da ‘yancin cin gashin kan, ta bangaren harkokin kudi da dabarun siyasa da gwamnatocin jihohin ke yi.

Har ila yau, ya yi zargin cewa; gwamnonin sun jajirce wajen nuna adawarsu ga ‘yancin cin gashin kan kananan hukumomin tare da kawo cikas ga samun kudadensu, duk da hukuncin da kotun kolin ta yanke a 2024.

“Babu wani abu da zai hana aiwatar da wannan hukunci, sai gwamnonin da suka yi wa ‘yan Nijeriya damfara ta hanyar yin awon gaba da kudaden kananan hukumomi. Ba wata tangardar doka ba ce, illa kawai dai tsantsar adawa ta siyasa, kamar yadda shugaban ya bayyana wa LEADERSHIP.

Kotun koli ta yanke shari’a a shekarar da ta gabata tare da bayar da umarnin a biya kudaden da ake ware wa kananan hukumomi kai tsaye a cikin asusunsu, domin kauce wa katsalandan din gwamnatin jihohi. Sai dai, bayan shekara guda cif da yanke hukuncin, Kankara ya koka da yadda ba a aiwatar da hukuncin ba, musamman saboda rashin kishi daga hukumomin jihohi da na kuma tarayya.

Wannan dalili ne a cewar tasa, ya jefa kananan hukumomi cikin mawuyacin hali da kuma kunci.

Cikin takaicin jinkirin da ake yi, shugaban NULGE ya bayyana cewa; kungiyar za ta kara kaimi wajen ganin an aiwatar da hukuncin kotun kolin.

Kankara ya bayyana cewa, kungiyar za ta ci gaba da yin fafutuka tare da kulla alaka mai karfi da kungiyoyi masu zaman kansu da hukumomin kasa da kasa da kuma kungiyar kwadago ta Nijeriya (NLC), domin matsa wa gwamnatin tarayya lamba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma
Labarai

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal
Labarai

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba

Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba

LABARAI MASU NASABA

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025
Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.