ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yankin Arewa Maso Gabashin Nijeriya Na Bukatar Agajin Gaggawa – MDD

by Sadiq
4 years ago
Arewa

Ofishin Majalisar Dinkin Duniya mai kula da ayyukan jin kai a Nijeriya, ya bayyana cewa har yanzu ba a shawo kan matsalar jin kai a yankin Arewa maso Gabas ba, yayin da mata da kananan yara suka rasa muhallansu a shekarar 2022.

A cewar rahoton Majalisar Dinkin Duniya a cikin 2023, miliyoyin mutane a Njjeriya za su ci gaba da fuskantar talauci, yayin da da dama kuma za su yi ta fadi tashin neman abinci.

  • An Kaddamar Da Ginin Sabuwar Hedikwatar Kungiyar ECOWAS
  • Tura Mu Aka Yi Mu Sace Sanatan APC- Wasu ‘Yan Bindiga Da Suka Shiga Hannu

Arewa maso gabashin Nijeriya ya kasance daya daga cikin manyan matsalolin jin kai a duniya, inda akalla mutane sama da miliyan takwas ke bukatar agaji a shekarar 2023.

ADVERTISEMENT

Matsalolin da mata da maza da yara ke fama da su a kowace rana a fadin Jihohin Borno da Adamawa da Yobe har yanzu na karuwa, a cewar rahoton.

Majalisar Dinkin Duniya ta ce, ana bukatar kusan Dala biliyan 1.2 domin tallafawa mutane miliyan 5.4 a fadin Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Rahoton ya ci gaba da cewa, a shekarar 2023, mutane miliyan 339 a fadin duniya za su bukaci agajin jin kai, wanda ya karu da kusan kashi 24 cikin dari idan aka kwatanta da bara.

Rahoton ya kara da cewa bukatun jin kai sun karu matuka saboda yakin da ake yi a Kasar Ukraine da kuma tasirin matsalar sauyin yanayi a yankin Gabashin Afirka da yankin Sahel da Pakistan da kuma Nijeriya.

“A yankin Yamma da Tsakiyar Afirka kadai, ana sa ran mutane miliyan 69 za su bukaci agajin jin kai a shekarar 2023, inda ake fargabar cewa Arewa maso Gabashin Nijeriya da Burkina Faso, wadanda ke fama da matsananciyar yunwa, za su iya shiga cikin mummunan yanayi, musamman idan matsalar sauyin yanayi ta tsananta,” in ji Majalisar Dinkin Duniya.

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Kashe ‘Yansanda 3 Da Wasu A Sakkwato 

'Yan Bindiga Sun Kashe 'Yansanda 3 Da Wasu A Sakkwato 

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.