• Leadership Hausa
Monday, February 6, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe ‘Yansanda 3 Da Wasu A Sakkwato 

by Sadiq
2 months ago
in Manyan Labarai
0
‘Yan Bindiga Sun Kashe ‘Yansanda 3 Da Wasu A Sakkwato 

Wasu da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne, a jiya da yamma, sun kai farmaki kauyen ‘Yarbulutu da ke karamar hukumar Sabon Birni a Jihar Sakkwato, inda suka kashe ‘yansanda uku tare da wasu ‘yan kasuwa uku.

Harin ya faru ne da misalin karfe 2:30 na rana a lokacin da shugaban kasa Muhammadu Buhari da ministan tsaro Salihi Magashi ke Sakkwato suna halartar taron shekara-shekara na COAS na 2022.

  • Yankin Arewa Maso Gabashin Nijeriya Na Bukatar Agajin Gaggawa – MDD
  • Fitacciyar Mawakiya Ta Jamhuriyar Nijar Hamsou Garba Ta Rasu

A cewar wani shaidan gani da ido, ‘yan bindigar da suka zo kan babura sun bude wuta kan ‘yan kasuwar da ba su ji ba ba su gani ba a kasuwar mako-mako, lamarin da ya sanya mutane tserewa, inda suka yi kaca-kaca da kasuwar

Jami’an ‘yansandan da ke wani shingen binciken ababen hawa sun garzaya wurin da ‘yan bindigar nan take suka kashe ‘yansanda uku tare da kone wasu motoci guda biyu.

Da yake tabbatar da harin, kakakin rundunar ‘yansandan Jihar Sakkwato, DSP Sanusi Abubakar, ya ce rundunar ta samu rahoton kuma suna farautar maharan domin fuskantar shari’a.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kama Wani Da Kokon Kan Mutum A Neja

‘Yan Bindiga Sun Kashe Alkali A Kotu A Jihar Imo

Wani mazaunin kauyen da lamarin ya faru a kan idonsa ya bayyana damuwarsa kan yadda ‘yan bindiga ke ta’addanci a yankin a kullum ba tare da wata turjiya ba.

Ya ce an dade ana tsare da kananan hukumomin Sabon Birni da Isa da ke gabashin Sakkwato domin karbar kudin fansa daga ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane da ke aiki a Zamfara da kuma wani bangare na Jihar Sakkwato.

“Na tabbata wadannan ‘yan bindigar sun fito ne daga Jihar Zamfara kuma yanzu sun koma yankinmu kamar yadda yankin ke da iyaka da jihar a gabas,” in ji ganau.

Idan ba a manta ba a makon jiya ne wasu ‘yan bindiga suka kai hari tare da kashe mutane shida a wani kauye na karamar hukumar Goronyo a jihar.

Irin wannan al’amari ya faru a farkon shekarar da ta gabata inda wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kashe sama da mutane 40.

Tags: 'YansandaSabon BirniSakkwatoYan bindiga
Previous Post

Yankin Arewa Maso Gabashin Nijeriya Na Bukatar Agajin Gaggawa – MDD

Next Post

Ban Taba Nadamar Kai Kara Kotu Kan Takarata Ba – Machina

Related

‘Yansanda Sun Kama Wani Da Kokon Kan Mutum A Neja
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Da Kokon Kan Mutum A Neja

1 day ago
‘Yan Bindiga Sun Kashe Alkali A Kotu A Jihar Imo
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Alkali A Kotu A Jihar Imo

1 day ago
Ba Za A Kara Tsawaita Wa’adin Daina Karbar Tsofaffin Takardun Kudi Ba —Emefiele
Manyan Labarai

Ba Za A Kara Tsawaita Wa’adin Daina Karbar Tsofaffin Takardun Kudi Ba —Emefiele

1 day ago
Akwai  Wasu Kusoshi A Fadar Shugaban Kasa Da Ke Goyon Bayan Atiku – Wike
Manyan Labarai

Akwai  Wasu Kusoshi A Fadar Shugaban Kasa Da Ke Goyon Bayan Atiku – Wike

2 days ago
Canjin Kudi: Ina Sane Da Wahalar Da Mutane Ke Sha, Komai Zai Daidaita – Buhari
Manyan Labarai

Canjin Kudi: Ina Sane Da Wahalar Da Mutane Ke Sha, Komai Zai Daidaita – Buhari

2 days ago
Gwamnonin APC Sun Gana Da Buhari Kan Bukatar Cire Wa’adin Karbar Tsofaffin Kudi
Manyan Labarai

Gwamnonin APC Sun Gana Da Buhari Kan Bukatar Cire Wa’adin Karbar Tsofaffin Kudi

2 days ago
Next Post
Ban Taba Nadamar Kai Kara Kotu Kan Takarata Ba – Machina

Ban Taba Nadamar Kai Kara Kotu Kan Takarata Ba - Machina

LABARAI MASU NASABA

Afirka Ba Ta Bukatar Lakca

Afirka Ba Ta Bukatar Lakca

February 5, 2023
Manoman Kwakwa 50 Sun Samu Horo Kan Noman Zamani

Manoman Kwakwa 50 Sun Samu Horo Kan Noman Zamani

February 5, 2023
Sin Na Matukar Adawa Da Matakin Amurka Na Harbo Babban Balan-balan Din Kasar Sin

Sin Na Matukar Adawa Da Matakin Amurka Na Harbo Babban Balan-balan Din Kasar Sin

February 5, 2023
Dalilan Da Ke Hana Kwamfuta Da Wayoyin Hannu Sauri

Dalilan Da Ke Hana Kwamfuta Da Wayoyin Hannu Sauri

February 5, 2023
Ko Mafarkin Samun Gwamna Mace Ta Farko A Nijeriya Zai Zama Gaskiya?

Ko Mafarkin Samun Gwamna Mace Ta Farko A Nijeriya Zai Zama Gaskiya?

February 5, 2023
Shirin Fim Na Tallata Shagalin Murnar Bikin Kunna Fitilu Da CMG Ya Tsara Ya Jawo Hankulan Al’ummar Afirka

Shirin Fim Na Tallata Shagalin Murnar Bikin Kunna Fitilu Da CMG Ya Tsara Ya Jawo Hankulan Al’ummar Afirka

February 5, 2023
An Gudanar Da Jerin Ayyuka Don Murnar Cika Shekara 1 Da Samun Nasarar Gudanar Da Wasannin Olympics Na Lokacin Sanyi Na Beijing

An Gudanar Da Jerin Ayyuka Don Murnar Cika Shekara 1 Da Samun Nasarar Gudanar Da Wasannin Olympics Na Lokacin Sanyi Na Beijing

February 5, 2023
NAHCON Ta Rarraba Kujerun Aikin Hajjin Bana Ga Jihohi 36 Da Abuja

NAHCON Ta Rarraba Kujerun Aikin Hajjin Bana Ga Jihohi 36 Da Abuja

February 5, 2023
Matar Sufeto Ta Gurfanar Da Kurtun Dan Sanda A Kotu Kan Kashe Mijinta

Ya Kashe Makocinsa Don Ya Haske Idon Mahaifiyarsa Da Cocila

February 5, 2023
Gwamnan Jigawa Ya Nada Hameem Nuhu Sanusi Matsayin Sabon Sarkin Dutse

Gwamnan Jigawa Ya Nada Hameem Nuhu Sanusi Matsayin Sabon Sarkin Dutse

February 5, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.