ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kashe ‘Yansanda 3 Da Wasu A Sakkwato 

by Sadiq
4 years ago
'Yansanda

Wasu da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne, a jiya da yamma, sun kai farmaki kauyen ‘Yarbulutu da ke karamar hukumar Sabon Birni a Jihar Sakkwato, inda suka kashe ‘yansanda uku tare da wasu ‘yan kasuwa uku.

Harin ya faru ne da misalin karfe 2:30 na rana a lokacin da shugaban kasa Muhammadu Buhari da ministan tsaro Salihi Magashi ke Sakkwato suna halartar taron shekara-shekara na COAS na 2022.

  • Yankin Arewa Maso Gabashin Nijeriya Na Bukatar Agajin Gaggawa – MDD
  • Fitacciyar Mawakiya Ta Jamhuriyar Nijar Hamsou Garba Ta Rasu

A cewar wani shaidan gani da ido, ‘yan bindigar da suka zo kan babura sun bude wuta kan ‘yan kasuwar da ba su ji ba ba su gani ba a kasuwar mako-mako, lamarin da ya sanya mutane tserewa, inda suka yi kaca-kaca da kasuwar

ADVERTISEMENT

Jami’an ‘yansandan da ke wani shingen binciken ababen hawa sun garzaya wurin da ‘yan bindigar nan take suka kashe ‘yansanda uku tare da kone wasu motoci guda biyu.

Da yake tabbatar da harin, kakakin rundunar ‘yansandan Jihar Sakkwato, DSP Sanusi Abubakar, ya ce rundunar ta samu rahoton kuma suna farautar maharan domin fuskantar shari’a.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

Wani mazaunin kauyen da lamarin ya faru a kan idonsa ya bayyana damuwarsa kan yadda ‘yan bindiga ke ta’addanci a yankin a kullum ba tare da wata turjiya ba.

Ya ce an dade ana tsare da kananan hukumomin Sabon Birni da Isa da ke gabashin Sakkwato domin karbar kudin fansa daga ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane da ke aiki a Zamfara da kuma wani bangare na Jihar Sakkwato.

“Na tabbata wadannan ‘yan bindigar sun fito ne daga Jihar Zamfara kuma yanzu sun koma yankinmu kamar yadda yankin ke da iyaka da jihar a gabas,” in ji ganau.

Idan ba a manta ba a makon jiya ne wasu ‘yan bindiga suka kai hari tare da kashe mutane shida a wani kauye na karamar hukumar Goronyo a jihar.

Irin wannan al’amari ya faru a farkon shekarar da ta gabata inda wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kashe sama da mutane 40.

MASU ALAKA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
Manyan Labarai

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Next Post
Ban Taba Nadamar Kai Kara Kotu Kan Takarata Ba – Machina

Ban Taba Nadamar Kai Kara Kotu Kan Takarata Ba - Machina

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.