• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

 ‘Yansanda Sun Cafke Wadanda Suka Kulle Matashi A Kejin Kare

by Rabi'u Ali Indabawa
6 months ago
in Labarai
0
 ‘Yansanda Sun Cafke Wadanda Suka Kulle Matashi A Kejin Kare
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani yaro Samuel Onyeme mai shekaru 17 ya sha dukan tsiya tare da kulle shi a cikin kejin kare saboda ya ziyarci wata abokiyar karatunsu, Miss Anastasia Celestine.

PUNCH Metro ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne a lokacin da Onyeme ya ziyarci abokiyar karatunsa a gidanta da misalin karfe 6 na yamma.

  • Mai Keta Hakkin Bil Adam Na Ikirarin Kare Shi
  • Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekara-shekara Don Bayyana Kokarinta Na Kare Hakkin Dan Adam

Mahaifiyar yaro, Misis Onyeme, ta shaida wa wakilinmu cewa ya fi kyau ta samu kyakkyawar tarba a gidan Mista Celestine.

Ta ce, “Dana Samuel, dan shekara 17 a duniya yana karatu a Babbar Sakandaren Redeemers International High School, Asaba, Jihar Delta, ya ziyarci abokiyar karatunsa, Anastasia Celestine, a gidanta bayan ta gayyace shi.

“Dana ya ce suna tattaunawa a wajen gidan Mista Celestine lokacin da mahaifinta da ’ya’yansa maza biyu suka hau shi da duka yi masa mugun rauni, ya ce sun yi amfani da katako sannan suka kulle shi a cikin kejin kare.

Labarai Masu Nasaba

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

“Sun kwace wayarsa suka kira ni (mahaifiya), da isowata, na yi kokarin ganinsa amma suka hana ni ganinsa na tsawon awanni biyu.”

Ta ce ‘yarta Jessica, wacce ke waje tana kokarin neman taimako, ita ma ‘yan gidan Celestine sun fuskanci hari a lokacin da ta yi kokarin sake shiga harabar gidan.

“Al’amarin ya ta’azzara sa’ad da Ben, dayan ’ya’yana, wanda shi ne dan’uwa ga Samuel, ya tuntubi wani abokinsa, wanda kuma ya yi magana da wata kungiyar kare hakkin bil’adama kafin su kai ga ’yan sanda, sai aka tara jami’ansu don ceto Samuel daga kejin kare, misalin karfe 10:00 na dare.”

Da yake karin haske, wani mai rajin kare hakkin bil’adama, Mista Bictor Ojei, wanda ya kai rahoton faruwar lamarin ga rundunar ‘yan sandan Jihar Delta a ranar Talata, ya ce ya tattara ‘yan sanda kafin a kubutar da Samuel daga kejin kare, ya kuma bayyana lamarin a matsayin dabbanci da rashin tausayi.

Ojei, a cikin wata takardar koke ga kwamishinan ‘yan sandan Jihar Delta, ya bukaci da a gaggauta gudanar da bincike tare da gurfanar da Mista Celestine da ‘ya’yansa maza bisa laifin yin garkuwa da su, tsarewa ba bisa ka’ida ba, cin zarafi, da yunkurin kisan kai bisa tanadin dokar laifuffuka ta Nijeriya.

Koken dai ya mika kwafi ga babban Lauyan Ma’aikatar Shari’a ta Jihar Delta a Asaba da kuma Kodinetan Hukumar Kare Hakkokin Dan’Adam ta kasa reshen Asaba Jihar Delta, inda ta bukaci a yi adalci.

“Wani Onyeme Ben ya tuntubi wani abokinsa, wanda shi ma ya tuntubi kungiyarmu. Bayan rahoton da muka samu ga rundunar ‘yan sandan Jihar Delta, ta tattara jami’ai, kuma an ceto Master Onyeme Samuel daga kejin kare da misalin karfe 10:00 na dare.

“Bisa bayanan da ke sama, Mista Celestine da ‘ya’yansa sun aikata laifukan da suka hada da tsare Misis Onyeme Onome ba bisa ka’ida ba har na tsawon sa’o’i biyu ba tare da iznin ta ba, da kuma tsare Master Onyeme Samuel a cikin kejin kare daga karfe 6:00 na yamma zuwa 10 na dare wanda ya saba wa sashe na 364 na dokar laifuka.

An ruwaito cewa wanda lamarin ya shafa, Samuel, a yanzu haka yana karbar magani a Asibitin kwararru na Asaba, sakamakon raunukan da ya samu yayin da lamarin ya faru.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DogKare
ShareTweetSendShare
Previous Post

’Yan Bindiga Sun Sace ’Yan Uwan Ɗan Jarida a Kogi, Sun Nemi Fansar Naira Miliyan 50

Next Post

Farfesa Zaynab Alkali: Mace Ta Farko Da Ta Zama Marubuciyar Littattafai Daga Arewacin Nijeriya

Related

Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno
Manyan Labarai

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

1 hour ago
Sanusi
Manyan Labarai

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

12 hours ago
Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 
Labarai

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

15 hours ago
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

16 hours ago
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus
Manyan Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

18 hours ago
Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

21 hours ago
Next Post
Farfesa Zaynab Alkali: Mace Ta Farko Da Ta Zama Marubuciyar Littattafai Daga Arewacin Nijeriya

Farfesa Zaynab Alkali: Mace Ta Farko Da Ta Zama Marubuciyar Littattafai Daga Arewacin Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

June 4, 2025
Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

June 3, 2025
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

June 3, 2025
Sanusi

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

June 3, 2025
Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

June 3, 2025
An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

June 3, 2025
Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

June 3, 2025
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.