• English
  • Business News
Thursday, July 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

 ‘Yansanda Sun Cafke Wadanda Suka Kulle Matashi A Kejin Kare

by Rabi'u Ali Indabawa
8 months ago
in Labarai
0
 ‘Yansanda Sun Cafke Wadanda Suka Kulle Matashi A Kejin Kare
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani yaro Samuel Onyeme mai shekaru 17 ya sha dukan tsiya tare da kulle shi a cikin kejin kare saboda ya ziyarci wata abokiyar karatunsu, Miss Anastasia Celestine.

PUNCH Metro ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne a lokacin da Onyeme ya ziyarci abokiyar karatunsa a gidanta da misalin karfe 6 na yamma.

  • Mai Keta Hakkin Bil Adam Na Ikirarin Kare Shi
  • Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekara-shekara Don Bayyana Kokarinta Na Kare Hakkin Dan Adam

Mahaifiyar yaro, Misis Onyeme, ta shaida wa wakilinmu cewa ya fi kyau ta samu kyakkyawar tarba a gidan Mista Celestine.

Ta ce, “Dana Samuel, dan shekara 17 a duniya yana karatu a Babbar Sakandaren Redeemers International High School, Asaba, Jihar Delta, ya ziyarci abokiyar karatunsa, Anastasia Celestine, a gidanta bayan ta gayyace shi.

“Dana ya ce suna tattaunawa a wajen gidan Mista Celestine lokacin da mahaifinta da ’ya’yansa maza biyu suka hau shi da duka yi masa mugun rauni, ya ce sun yi amfani da katako sannan suka kulle shi a cikin kejin kare.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Boko Haram Ibn Khalid A Borno

Tinubu Ya Tattauna da Gwamnonin APC Kafin Muhimmin Taron NEC

“Sun kwace wayarsa suka kira ni (mahaifiya), da isowata, na yi kokarin ganinsa amma suka hana ni ganinsa na tsawon awanni biyu.”

Ta ce ‘yarta Jessica, wacce ke waje tana kokarin neman taimako, ita ma ‘yan gidan Celestine sun fuskanci hari a lokacin da ta yi kokarin sake shiga harabar gidan.

“Al’amarin ya ta’azzara sa’ad da Ben, dayan ’ya’yana, wanda shi ne dan’uwa ga Samuel, ya tuntubi wani abokinsa, wanda kuma ya yi magana da wata kungiyar kare hakkin bil’adama kafin su kai ga ’yan sanda, sai aka tara jami’ansu don ceto Samuel daga kejin kare, misalin karfe 10:00 na dare.”

Da yake karin haske, wani mai rajin kare hakkin bil’adama, Mista Bictor Ojei, wanda ya kai rahoton faruwar lamarin ga rundunar ‘yan sandan Jihar Delta a ranar Talata, ya ce ya tattara ‘yan sanda kafin a kubutar da Samuel daga kejin kare, ya kuma bayyana lamarin a matsayin dabbanci da rashin tausayi.

Ojei, a cikin wata takardar koke ga kwamishinan ‘yan sandan Jihar Delta, ya bukaci da a gaggauta gudanar da bincike tare da gurfanar da Mista Celestine da ‘ya’yansa maza bisa laifin yin garkuwa da su, tsarewa ba bisa ka’ida ba, cin zarafi, da yunkurin kisan kai bisa tanadin dokar laifuffuka ta Nijeriya.

Koken dai ya mika kwafi ga babban Lauyan Ma’aikatar Shari’a ta Jihar Delta a Asaba da kuma Kodinetan Hukumar Kare Hakkokin Dan’Adam ta kasa reshen Asaba Jihar Delta, inda ta bukaci a yi adalci.

“Wani Onyeme Ben ya tuntubi wani abokinsa, wanda shi ma ya tuntubi kungiyarmu. Bayan rahoton da muka samu ga rundunar ‘yan sandan Jihar Delta, ta tattara jami’ai, kuma an ceto Master Onyeme Samuel daga kejin kare da misalin karfe 10:00 na dare.

“Bisa bayanan da ke sama, Mista Celestine da ‘ya’yansa sun aikata laifukan da suka hada da tsare Misis Onyeme Onome ba bisa ka’ida ba har na tsawon sa’o’i biyu ba tare da iznin ta ba, da kuma tsare Master Onyeme Samuel a cikin kejin kare daga karfe 6:00 na yamma zuwa 10 na dare wanda ya saba wa sashe na 364 na dokar laifuka.

An ruwaito cewa wanda lamarin ya shafa, Samuel, a yanzu haka yana karbar magani a Asibitin kwararru na Asaba, sakamakon raunukan da ya samu yayin da lamarin ya faru.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DogKare
ShareTweetSendShare
Previous Post

’Yan Bindiga Sun Sace ’Yan Uwan Ɗan Jarida a Kogi, Sun Nemi Fansar Naira Miliyan 50

Next Post

Farfesa Zaynab Alkali: Mace Ta Farko Da Ta Zama Marubuciyar Littattafai Daga Arewacin Nijeriya

Related

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Boko Haram Ibn Khalid A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Boko Haram Ibn Khalid A Borno

5 hours ago
Tinubu Ya Tattauna da Gwamnonin APC Kafin Muhimmin Taron NEC
Manyan Labarai

Tinubu Ya Tattauna da Gwamnonin APC Kafin Muhimmin Taron NEC

6 hours ago
Cutar Amai Da Gudawa Ta Hallaka Mutane 13 A Neja
Manyan Labarai

Cutar Amai Da Gudawa Ta Hallaka Mutane 13 A Neja

7 hours ago
Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!
Ra'ayi Riga

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

9 hours ago
An Yi Wa Ƴan Mata  Fiye Da 754,000 Rigakafin Cutar Sankarar Mahaifa
Labarai

An Yi Wa Ƴan Mata  Fiye Da 754,000 Rigakafin Cutar Sankarar Mahaifa

10 hours ago
Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne
Ra'ayi Riga

Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

10 hours ago
Next Post
Farfesa Zaynab Alkali: Mace Ta Farko Da Ta Zama Marubuciyar Littattafai Daga Arewacin Nijeriya

Farfesa Zaynab Alkali: Mace Ta Farko Da Ta Zama Marubuciyar Littattafai Daga Arewacin Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Boko Haram Ibn Khalid A Borno

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Boko Haram Ibn Khalid A Borno

July 23, 2025
An Kaddamar Da Bikin BIRTV2025 A Beijing

An Kaddamar Da Bikin BIRTV2025 A Beijing

July 23, 2025
Tinubu Ya Tattauna da Gwamnonin APC Kafin Muhimmin Taron NEC

Tinubu Ya Tattauna da Gwamnonin APC Kafin Muhimmin Taron NEC

July 23, 2025
Masu Zuba Jari Na Kasa Da Kasa Sun Gamsu Zuba Jari A Sin Dama Ce Ta Cimma Nasarar More Riba A Nan Gaba

Masu Zuba Jari Na Kasa Da Kasa Sun Gamsu Zuba Jari A Sin Dama Ce Ta Cimma Nasarar More Riba A Nan Gaba

July 23, 2025
Cutar Amai Da Gudawa Ta Hallaka Mutane 13 A Neja

Cutar Amai Da Gudawa Ta Hallaka Mutane 13 A Neja

July 23, 2025
Sin Ta Yi Mu’amala Da Kasashen Dake Kan Karshen Kogin Yarlung Zangbo Dangane Da Batun Gina Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Karfin Ruwa A Kogin

Sin Ta Yi Mu’amala Da Kasashen Dake Kan Karshen Kogin Yarlung Zangbo Dangane Da Batun Gina Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Karfin Ruwa A Kogin

July 23, 2025
Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa

Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa

July 23, 2025
Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

July 23, 2025
An Yi Wa Ƴan Mata  Fiye Da 754,000 Rigakafin Cutar Sankarar Mahaifa

An Yi Wa Ƴan Mata  Fiye Da 754,000 Rigakafin Cutar Sankarar Mahaifa

July 23, 2025
Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

July 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.