• English
  • Business News
Sunday, May 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

 ‘Yansanda Sun Cafke Wadanda Suka Kulle Matashi A Kejin Kare

by Rabi'u Ali Indabawa
6 months ago
in Labarai
0
 ‘Yansanda Sun Cafke Wadanda Suka Kulle Matashi A Kejin Kare
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani yaro Samuel Onyeme mai shekaru 17 ya sha dukan tsiya tare da kulle shi a cikin kejin kare saboda ya ziyarci wata abokiyar karatunsu, Miss Anastasia Celestine.

PUNCH Metro ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne a lokacin da Onyeme ya ziyarci abokiyar karatunsa a gidanta da misalin karfe 6 na yamma.

  • Mai Keta Hakkin Bil Adam Na Ikirarin Kare Shi
  • Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekara-shekara Don Bayyana Kokarinta Na Kare Hakkin Dan Adam

Mahaifiyar yaro, Misis Onyeme, ta shaida wa wakilinmu cewa ya fi kyau ta samu kyakkyawar tarba a gidan Mista Celestine.

Ta ce, “Dana Samuel, dan shekara 17 a duniya yana karatu a Babbar Sakandaren Redeemers International High School, Asaba, Jihar Delta, ya ziyarci abokiyar karatunsa, Anastasia Celestine, a gidanta bayan ta gayyace shi.

“Dana ya ce suna tattaunawa a wajen gidan Mista Celestine lokacin da mahaifinta da ’ya’yansa maza biyu suka hau shi da duka yi masa mugun rauni, ya ce sun yi amfani da katako sannan suka kulle shi a cikin kejin kare.

Labarai Masu Nasaba

2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

“Sun kwace wayarsa suka kira ni (mahaifiya), da isowata, na yi kokarin ganinsa amma suka hana ni ganinsa na tsawon awanni biyu.”

Ta ce ‘yarta Jessica, wacce ke waje tana kokarin neman taimako, ita ma ‘yan gidan Celestine sun fuskanci hari a lokacin da ta yi kokarin sake shiga harabar gidan.

“Al’amarin ya ta’azzara sa’ad da Ben, dayan ’ya’yana, wanda shi ne dan’uwa ga Samuel, ya tuntubi wani abokinsa, wanda kuma ya yi magana da wata kungiyar kare hakkin bil’adama kafin su kai ga ’yan sanda, sai aka tara jami’ansu don ceto Samuel daga kejin kare, misalin karfe 10:00 na dare.”

Da yake karin haske, wani mai rajin kare hakkin bil’adama, Mista Bictor Ojei, wanda ya kai rahoton faruwar lamarin ga rundunar ‘yan sandan Jihar Delta a ranar Talata, ya ce ya tattara ‘yan sanda kafin a kubutar da Samuel daga kejin kare, ya kuma bayyana lamarin a matsayin dabbanci da rashin tausayi.

Ojei, a cikin wata takardar koke ga kwamishinan ‘yan sandan Jihar Delta, ya bukaci da a gaggauta gudanar da bincike tare da gurfanar da Mista Celestine da ‘ya’yansa maza bisa laifin yin garkuwa da su, tsarewa ba bisa ka’ida ba, cin zarafi, da yunkurin kisan kai bisa tanadin dokar laifuffuka ta Nijeriya.

Koken dai ya mika kwafi ga babban Lauyan Ma’aikatar Shari’a ta Jihar Delta a Asaba da kuma Kodinetan Hukumar Kare Hakkokin Dan’Adam ta kasa reshen Asaba Jihar Delta, inda ta bukaci a yi adalci.

“Wani Onyeme Ben ya tuntubi wani abokinsa, wanda shi ma ya tuntubi kungiyarmu. Bayan rahoton da muka samu ga rundunar ‘yan sandan Jihar Delta, ta tattara jami’ai, kuma an ceto Master Onyeme Samuel daga kejin kare da misalin karfe 10:00 na dare.

“Bisa bayanan da ke sama, Mista Celestine da ‘ya’yansa sun aikata laifukan da suka hada da tsare Misis Onyeme Onome ba bisa ka’ida ba har na tsawon sa’o’i biyu ba tare da iznin ta ba, da kuma tsare Master Onyeme Samuel a cikin kejin kare daga karfe 6:00 na yamma zuwa 10 na dare wanda ya saba wa sashe na 364 na dokar laifuka.

An ruwaito cewa wanda lamarin ya shafa, Samuel, a yanzu haka yana karbar magani a Asibitin kwararru na Asaba, sakamakon raunukan da ya samu yayin da lamarin ya faru.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DogKare
ShareTweetSendShare
Previous Post

’Yan Bindiga Sun Sace ’Yan Uwan Ɗan Jarida a Kogi, Sun Nemi Fansar Naira Miliyan 50

Next Post

Farfesa Zaynab Alkali: Mace Ta Farko Da Ta Zama Marubuciyar Littattafai Daga Arewacin Nijeriya

Related

2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC
Labarai

2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

22 minutes ago
Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar
Manyan Labarai

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

4 hours ago
Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne
Labarai

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

6 hours ago
Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)
Labarai

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

7 hours ago
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari
Labarai

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

8 hours ago
Labarai

Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu

20 hours ago
Next Post
Farfesa Zaynab Alkali: Mace Ta Farko Da Ta Zama Marubuciyar Littattafai Daga Arewacin Nijeriya

Farfesa Zaynab Alkali: Mace Ta Farko Da Ta Zama Marubuciyar Littattafai Daga Arewacin Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

May 11, 2025
Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

May 11, 2025
Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

May 11, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

May 11, 2025
Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

May 11, 2025
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

May 11, 2025
Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

May 11, 2025
Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

May 11, 2025
Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

May 11, 2025
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

May 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.