• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Cafke ‘Yan Fashin Daji 7, Sun Ceto Mutane 15

by Hussein Yero
3 years ago
in Manyan Labarai
0
‘Yansanda Sun Cafke ‘Yan Fashin Daji 7, Sun Ceto Mutane 15
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansandan Jihar Zamfara ta kama wasu mutane bakwai da ake zargi da aikata laifukan da suka shafi fashi da makami ciki har da mace mai kai wa ‘yan bindiga makamai.

Sannan sun samu nasarar kubutar da wasu mutane 15 da aka yi garkuwa da su bayan shafe kwanaki 50 a hannun masu garkuwan.

  • Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Yanke Wa Dan Takarar Gwamnan YPP Hukuncin Daurin Shekaru 42 A Akwa Ibom
  • Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Yanke Wa Dan Takarar Gwamnan YPP Hukuncin Daurin Shekaru 42 A Akwa Ibom

Kakakin Rundunar ‘Yansandan jihar, SP Muhammad Shehu, ne ya bayyana haka yayin da yake gabatar da wadanda ake zargin ga manema labarai a shelkwatar rundunar da ke Gusau a ranar Alhamis.

A cewarsa, an kama wasu mutane shida da ake zargi da laifin hada baki, da kuma tsoratarwa da karbar kudaden fansa a garuruwan yankin karamar hukumar Anka.

Wadanda ake zargin sun hada da, Jamilu Muhammad na kauyen Gadar Manya, Zayyanu Barmo na kauyen Manya Babba, Abubakar Usman na kauyen Mandau, Lauwali Girkau na kauyen Girkau, Sala Girkau na kauyen Girkau da Abubakar Yahaya na kauyen Tungar Mani.

Labarai Masu Nasaba

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

“Mutane shidan da ake zargin ‘yan fashi ne da ke sanya haraji a kan al’ummar da suke a garuruwan da yin garkuwa da su, inda suka tara miliyoyin Naira ta hanyar asusun banki da suka kirkira don haka.

“Bayan an yi musu tambayoyi, duk wadanda ake zargin sun amsa laifinsu sannan suka bayyana cewa suna aika wa da sakon barazana ga kauyukan ko dai su biya kudi ko kuma a kai musu hari sannan kuma sun amsa cewa sun karbi miliyoyin Naira daga wasu al’ummomi biyar.

“Ana ci gaba da gudanar da bincike mai zurfi da nufin kamo sauran wadanda ake zargi da hannu a wannan aika-aika,” in ji kakakin rundunar ‘yansandan.

Kazalika, rundunar ta kuma kama wata mata mai matsakaicin shekaru mai suna Gaje Abdullahi, ‘yar kauyen Madaci da ke Jihar Katsina bisa laifin safarar makamai da alburusai zuwa ga wani shahararren dan bindiga da ake kira Dawa wanda ya addabi jihohin Zamfara da Katsina.

Sai dai matar a wata hira da manema labarai ta amsa laifin ta, inda ta ce Dawa ne ya tilasta mata aikata wannan aika-aika saboda tsoron kada su afka mata kamar yadda suka yi wa mijinta suka kashe shi tare da jimata rauni a fuska.

Gaje ta bayyana cewa, shi Dawa aikenta ya yi ta amso masa gyada kuma har ya yi mata alkawarin zai ba ta tiya goma dan yin Kulikuli kuma ya bata naira dubu goma kudin Mota, “Ashe harsashin ne ya aikeni amso ba gyada ba ce.”

Har-ila-yau, ‘Yansanda sun ceto mutanan dajin sabon garin Dustin Kaura da ke gundumar Danjibga a karamar hukumar Tsafe wanda ya kai ga ceto mutanen da aka yi garkuwa da su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaBincikeKatsinaYan bindigaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

CMG Ya Lashe Lambobin Yabo 4 Na Watsa Shirye-shirye Na Gasar Wasannin Olympics Ta Beijing 2022

Next Post

Shugaban Rikon Kwarya Na Chadi Na Son Zurfafa Hadin Gwiwa Tare Da Sin 

Related

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

11 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

13 hours ago
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

17 hours ago
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

18 hours ago
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja
Manyan Labarai

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

21 hours ago
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi
Daga Birnin Sin

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

1 day ago
Next Post
Shugaban Rikon Kwarya Na Chadi Na Son Zurfafa Hadin Gwiwa Tare Da Sin 

Shugaban Rikon Kwarya Na Chadi Na Son Zurfafa Hadin Gwiwa Tare Da Sin 

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

June 27, 2025
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

June 27, 2025
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

June 27, 2025
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.