ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

by Sadiq
3 months ago
'Yansanda

’Yansanda a Abuja sun kama wasu shugabannin ƙungiyar masu garkuwa da mutane bayan wani samame na musamman da suka kai.

Waɗanda aka kama su ne Masud Abdullahi daga Karu, Jihar Nasarawa, wanda ake zargin shi ne shugaban ƙungiyar, da kuma Muhammad Tahir daga Jos, Jihar Filato.

  • Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 
  • Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

’Yansanda sun ce ƙungiyar ta daɗe tana addabar Abuja da kewaye da garkuwa da mutane.

ADVERTISEMENT

Kama su ya biyo bayan wani rahoto da aka samu a ranar 16 ga wata. Agusta, 2025, cewa wasu masu garkuwa sun kai hari wata unguwa a Karu, a Abuja.

Sun shiga gidan lauya Barista Henry Chichi, inda suka yi awo  gaba da shi.

LABARAI MASU NASABA

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Bayan kai rahoto wajen ’yansanda, rundunar yaƙi da garkuwa ta yi aiki, inda daga ƙarshe ta kuɓutar da wanda aka sace a ranar 17 ga wata  Agusta da misalin ƙarfe 9:05 na dare.

A wani samame da rundunar ’yansandan Jihar Nasarawa ta kai, jami’anta sun bi sawun masu garkuwa a kan titin Nasarawa zuwa Abuja, inda motarsu Opel Vectra ja ta kife a garin Guraku.

Wasu daga cikin ’yan ƙungiyar sun tsere, amma Abdullahi da Tahir an cafke su.

Daga baya, waɗanda aka kama sun kai ’yansanda maɓoyarsu da ke dajin Karshi a Nasarawa, inda aka kama wani ɗan ƙungiyar mai shekara 22, mai suna Kabiru Jibril.

Abubuwan da aka samu a maɓoyar sun haɗa da kuɗi Naira miliyan 7.4, bindigogi AK-47 guda uku, bindiga G3 guda ɗaya, harsasai guda 16 da wayar Tecno.

Kwamishinan ’Yansandan Abuja, Ajao Adewale, ya yaba da ƙwarewa da jarumtar jami’an rundunar, tare da tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Ya kuma ce suna ci gaba da bin sahun sauran ’yan ƙungiyar da suka tsere.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su
Manyan Labarai

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle
Manyan Labarai

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
Next Post
Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

LABARAI MASU NASABA

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.