ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Kama Mutumin Da Ya Kashe Matarsa A Adamawa

by Hussaini Hammangabdo, Yola
3 years ago
Adamawa

Rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa ta cafke wani magidanci mai suna Aminu Abubakar dan shekara 56 bisa laifin kashe matarsa.

Abubakar, mazaunin Lelewaji, Shagari Phase 2 a Yola, karamar hukumar Yola ta Kudu a jihar, ya yi zargin ya yi wa matarsa Nana Fadimatu dukan tsiya har lahira, bayan ta fahimci shirinta na auren wani.

  • ‘Yansanda Sun Kama Mutumin Da Ya Kashe Matarsa A Adamawa
  • Manyan Jami’an Kasashen Sin Da Amurka Sun Tattauna Game Da Alakar Kasashen Biyu

 Ana zargin Abubakar da saki marigayiyar har sau biyu tare da ba ta masauki ba, har zuwa lokacin da ake sa ran za a sasanta auren. Amma kafin su sasanta, an ce marigayiyar tana shirin auren wani mutum, lamarin da ya fusata Abubakar, inda ya shiga tashin hankali.

ADVERTISEMENT

 Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan (PPRP) a wata sanarwa da ya fitar, ya ce, “Wanda ake zargin, Aminu Abubakar, mazaunin Lelewaji, Shagari Phase 2, a Karamar Hukumar Yola ta Kudu, ya yi wa marigayiya Nana Fadimatu dukan tsiya bayan wata ‘yar rashin jituwa da ta da ke tsakaninsu lokacin da ya ji labarin cewa marigayiyar za ta auri sabon miji wata rana.

Wanda ake zargin ya fusata ne inda ya kai ga danne ta a ranar 5/5/2023 da misalin karfe 10 na dare, ya buga mata wani abu mai karfi da hakan ya sa ta fadi sumamme, sannan daga baya aka sanar da cewa ta mutu.

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

An Kama Sojoji Biyu A Legas Kan Alaka Da Sarrafa Magungunan Jabu

“’Yansanda sun kama wanda ake zargin ne a shelkwatar ‘yan sanda ta Shagari sakamakon rahoton da aka samu daga sabon mijin da zai aure Mahmud Rufa’i na Shagari Anned, da ke Karamar Hukumar Yola ta Kudu.

“Ya zuwa yanzu dai, bincike ya nuna cewa wanda ake zargin shi ne manajan kamfanin ruwa na Anasam a gidan Jambutu 50 yana da da daya tare da marigayiyar bayan shekaru 9 da aurensu. “Kwamishanan ‘yan sanda CP Afolabi Babatola yayin da yake nuna kaduwarsa kan lamarin ya yaba wa DPO Shagari bisa kama wanda ake zargin ya kuma ce lallai za a gurfanar da shi gaban kotu domin hukunta shi.”

 Ya kara da cewa CP din ya umurci jami’an sashen yaki da kashe-kashe masu alaka da CID na jihar da su dauki nauyin gudanar da bincike tare da tabbatar da doka ta yi aiki. Hakazalika ya yi kira ga jama’a da su rika kai rahoton mutane masu aikata munanan laifuka ga ‘yan sanda.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
An Kama Sojoji Biyu A Legas Kan Alaka Da Sarrafa Magungunan Jabu
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Sojoji Biyu A Legas Kan Alaka Da Sarrafa Magungunan Jabu

December 20, 2025
An Ceto Wasu Samari 11 ‘Yan Jihar Jigawa Daga Hannun Masu Fataucin Mutane
Kotu Da Ɗansanda

An Ceto Wasu Samari 11 ‘Yan Jihar Jigawa Daga Hannun Masu Fataucin Mutane

December 20, 2025
Next Post
Gwamnatin Tarayya Za Ta Daina Ciyar Da Fursunoni Abinci

Gwamnatin Tarayya Za Ta Daina Ciyar Da Fursunoni Abinci

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.