• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Yi Wa Jama’a Kutse A Asusun Banki

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Za A Sake Gurfanar Da Faston Da Ake Zargi Da Sa Mabiyansa Azumin Mutuwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

Shelkwatar rundunar ‘yansanda ta Zone 2 da ke Onikan a Legas ta fatattaki wata kungiya da ta yi kutse a asusun kwastomomi na banki tare da damfarar su miliyoyin kudade.

Tuni dai an kama wasu mutum biyu da ake zargi da hannu wajen zambar, yayin da ‘yansanda suka bayyana su a matsayin mambobin kungiyar.

  • Sin Ta Bukaci Japan Da Kada Ta Yi Yunkurin Amfani Da Rahoton IAEA A Matsayin Izinin Zubar Da Dagwalon Ruwan Nukiliya A Cikin Teku
  • Kasar Sin: Bai Kamata Japan Ta Dauki Rahoton IAEA A Matsayin Izinin Zuba Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Ba

A wata sanarwa da jami’ar hulda da jama’a ta rundunar ‘yansandan shiyyar (ZPPRO) wadda ta kunshi jihohin Legas da Ogun, SP Hauwa Idris Adamu, ta fitar, ta ce ’yan kungiyar sun damfari mutum sama da 1000, wadanda suka watsu a fadin kasar nan.

Da take ba da bayanin yadda aka yi nasarar tarwatsa su, Adamu, ta ce, a ranar 8 ga Mayu, 2023, bankin United Bank for Africa (UBA) ya gabatar da koke ga Mataimakin Sufeto Janar na ‘yansanda, Mista Ari Ari Mohammed Ali, cewa akwai wasu kungiyoyin da suka kware kan zamba ta intanet na bankuna daban-daban a Nijeriya musamman United Bank for Africa (UBA), inda suka yi kutse cikin asusun kwastomomi tare da kwashe kudadensu.

“Bisa ga takardar koke, AIG ya tada wata tawagar ‘yansanda daga sashen sa ido na shiyyar, wadanda suka shiga aiki tare da taimakon fasahar zamani, mutum biyu da ake zargi; Yusuf Ademola mai shekaru 40 da Adesina Olawale Abiodun, 50, an gano su ne a maboyarsu da ke Ijebu Ode a Jihar Ogun.

 “Wadanda ake zargin sun amsa laifin da ake zargin su da aikatawa, kuma sun ce suna da kungiyoyi da dama a ko ina cikin fadin Nijeriya, wadanda suke amfani da manhajojin kwamfuta wajen yin kutse a cikin asusun abokan hulda da kuma fitar da kudadensu ba tare da an gano su daga bankin da suke so ba.

 “Duk da haka, tsarin da wadannan ‘yan damfara ke amfani da su shi ne samun lambar wayar abokin ciniki ta BBN da kuma sanarwar banki domin a samu saukin cire kudin.

Sakamakon haka, an yi kutse tare da zamba a asusun abokan ciniki sama da 1000 a duk fadin kasar nan. “Binciken da aka yi a kan lamarin ya nuna cewa an fito da ‘yan kungiyar ne daga sassa daban-daban na kasar nan, ana kuma kokarin kamo sauran wadanda ake zargi da hannu a wannan aika-aika.

“A cikin aiki na wucin gadi, ana ci gaba da bincike kuma nan ba da jimawa ba za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu bayan kammala bincike.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YasandaAikaa-AikaKotu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Gombe Ta Bukaci Jami’an Lafiya Da Su Kara Kwazo Wajen Yaki Da Cutar Sida

Next Post

Hanyoyin Magance Amosanin (Dandruff)

Related

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

3 weeks ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

3 weeks ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

3 weeks ago
An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

4 weeks ago
Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara
Kotu Da Ɗansanda

Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara

4 weeks ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi Tare Da Kwato Makamai A Delta

4 weeks ago
Next Post
Hanyoyin Magance Amosanin (Dandruff)

Hanyoyin Magance Amosanin (Dandruff)

LABARAI MASU NASABA

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.