• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yanzu-yanzu: Hon. Buba Mashio Ya Zama Sabon Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Yobe

by Muhammad Maitela
2 years ago
in Labarai
0
Yanzu-yanzu: Hon. Buba Mashio Ya Zama Sabon Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Yobe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hon. Chiroma Buba Mashio daga mazabar Jajere, ya zama sabon Kakakin majalisar dokokin jihar Yobe, karo na 8.

 

Hakan ya biyo bayan zaman da majalisar ta kaddamar yau a zauren majalisar dake Damaturu, yayin da aka fara gabatar da kudirin zaben sabon Kakakin Majalisar, wanda Hon. Adamu Dala Dogo mai wakiltar mazabar Karasuwa ya gabatar inda ya samu goyon bayan Hon. Bukar Mustapha na mazabar Geidam ta tsakiya tare da samun amincewar dukkanin yan majalisar dokokin 24.

  • Siyasa: Tsugune Ba Ta Kare Wa Tinubu Ba A Kotun Sauraren Kararrakin Zabe

An haifi Hon. Buba Mashio ranar 25 ga Mayu, a 1968 a garin Mashio a karamar hukumar Fune dake jihar Yobe.

 

Labarai Masu Nasaba

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Ya fara karatun sa a firamaren Mashio sannan ya wuce Sakandaren Gwamnati dake Damagum, kuma ya fara aiki a karamar hukumar Fune inda ya yi murabus ya tsaya takarar kansila mai wakiltar gundumar Mashio, inda daga bisani ya zama mataimakin shugaban karamar hukumar.

 

A kokarinsa na cigaba da karatunsa, sabon Kakakin ya garzaya inda yayi Diploma a Ramat Polytechnic Maiduguri, da Digirinsa na farko a Jami’ar Maiduguri a fannin kimiyyar siyasa.

 

Mashio ya tsaya takarar dan majalisar dokokin jihar Yobe mai wakiltar mazabar Jajere a 1999, ya yi aiki a kwamitoci da mukamai daban-daban a zauren majalisar.

 

Sauran manyan kusoshin majalisar sun hada da mataimakin Kakakin majalisar, Hon. Yau Usman Dachia, Shugaban Majalisar, Hon. Nasiru Hassan Yusuf, Mataimakinsa, Hon. Hassan Muhd ​​Yusufari, Mai.Tsawatarwa a zauren majalisar, Hon. Muhammed Auwal Isa Bello, mataimakinsa, Hon. Ahmed Musa Dumbu.

 

A jawabinsa na godiya, sabon Kakakin majalisar, Chiroma Buba Mashio ya bayyana jin dadinsa ga takwarorinsa bisa ga damar da suka bashi ya jagoranci zauren majalisar na 8, tare da daukacin al’ummar jihar baki daya.

 

Mashio ya yi alkawarin samar da ingantaccen shugabanci “ba tare da nuna son kai ba; tsarin mulkin Tarayyar Nijeriya zai jagorance ni. Zan aiwatar da manufar bude kofa don maraba da shawarwari don inganta shugabanci nagari don samar da ingantacciyar doka.

 

Shugaban majalisar ya bada tabbacin yin aiki cikin kwanciyar hankali da bangaren zartaswa da bangaren shari’a domin a samar da shugabanci nagari a jihar Yobe.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bikin Sallar Layya: Gwamnatin Katsina Ta Ayyana Hutun Mako Guda Ga Makarantu

Next Post

Gwamnatin Kano Za Ta Sake Gina Shatale-talen Gidan Gwamnati Da Aka Rusa A Wajen Birnin Jihar

Related

Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

8 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

8 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

9 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

9 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

12 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

13 hours ago
Next Post
Gwamnatin Kano Za Ta Sake Gina Shatale-talen Gidan Gwamnati Da Aka Rusa A Wajen Birnin Jihar

Gwamnatin Kano Za Ta Sake Gina Shatale-talen Gidan Gwamnati Da Aka Rusa A Wajen Birnin Jihar

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.