• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yanzu Yanzu – Kotu Ta Soke Zaɓen Ƙananan Hukumomn Ribas

by Abubakar Sulaiman
5 months ago
in Manyan Labarai
0
Yanzu Yanzu – Kotu Ta Soke Zaɓen Ƙananan Hukumomn Ribas
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kotun Ƙoli ta bayyana cewa zaɓen ƙananan hukumomi da aka gudanar a Jihar Rivers a ranar 5 ga Oktoba, 2024, ba shi da inganci, kuma ya saɓa wa doka. Kotun ta yanke hukuncin cewa zaɓen ya kasance haramtacce, kuma saboda rashin bin ƙa’idojin da doka ta tanada kafin gudanar da irin wannan zaɓe.

A cewar kotun, hukumar zabte ta Jihar Rivers (RSIEC) ta karya dokokin gudanar da zabe, inda ta saɓa wa sashi na 150 na dokar zaɓe ta 2022.

A baya dai, wata babbar kotu a Abuja ta hana hukumar zabe ta ƙasa (INEC) bayar da rajistar masu kaɗa ƙuri’a ga RSIEC domin gudanar da zaɓen, bisa hujjar cewa ba a cika sharuɗɗan gudanar da zaɓe ba. Haka kuma, kotun ta hana Sufeto Janar na ‘Yansanda da hukumar tsaro ta DSS samar da tsaro yayin zaɓen, domin gujewa duk wata matsala da ka iya tasowa. Wannan umarni ya biyo bayan ƙarar da jam’iyyar APC ta shigar, tare da rakiyar lauyoyinta Joseph Daudu, Sebastine Hon, da Ogwu James Onoja, dukkaninsu SAN.

  • Shugaban NPA Ya Kai Ziyarar Neman Masu Zuba Jari A Tashoshin Jiragen Ruwa Na Onne Da Ta Jihar Ribas
  • Jam’iyyar APC Ta Sahalewa Shugaba Tinubu Damar Neman Shugabancin Nijeriya A 2027

Kotun ta bayyana cewa RSIEC ta yi kuskure wajen sanya ranar zaɓe ba tare da bin dokokin da suka wajaba ba, ciki har da rashin sanar da jama’a kwanaki 90 kafin a gudanar da zaɓen, kamar yadda doka ta tanada. Haka kuma, an gaza sabunta da tantance rajistar masu kaɗa kuri’a, wanda hakan ya saɓa wa ƙa’idar zaɓe. Saboda haka, kotun ta ayyana cewa zaben bai cika ƙa’idojin doka ba, kuma ba za a amince da sakamakonsa ba.

Bugu da ƙari, kotun ta haramta amfani da rajistar masu kaɗa ƙuri’a da INEC ta tanadar, har sai an cika dukkan sharuddan da doka ta tanada. Wannan hukunci na kotu yana nufin cewa duk wanda aka zaɓa a ƙarƙashin wannan zaɓe ba zai ci gaba da riƙe muƙaminsa ba.

Labarai Masu Nasaba

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

Tinubu Ya Nada Ɗan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

Wannan mataki yana da matuƙar tasiri a siyasar Jihar Ribas, inda jam’iyyar APP ce ta lashe mafi yawan kujeru a zaɓen da aka soke.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ElectionZaɓe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Duk Da Hukuncin Kotun Koli, Har Yanzu Kananan Hukumomi Sun Gaza Samun Cikakken ‘Yanci

Next Post

Ka Cire Sarkin Kano Bayero Daga Fadar Nasarawa – Gwamnatin Kano Ga Tinubu

Related

APC
Manyan Labarai

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

8 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nada Ɗan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

22 hours ago
Sojoji Sun Daƙile Wani Harin Ta’addanci Tare Da Cafke Wasu Mutum Biyu A Taraba
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Wani Harin Ta’addanci Tare Da Cafke Wasu Mutum Biyu A Taraba

1 day ago
Buhari 1942 – 2025: Rayuwarsa, Rasuwarsa, Jana’izarsa, Da Ci gaba Da Ta’aziyya
Manyan Labarai

Buhari 1942 – 2025: Rayuwarsa, Rasuwarsa, Jana’izarsa, Da Ci gaba Da Ta’aziyya

1 day ago
Natasha Ta Rubuta Wa Majalisa, Tana Neman A Yi Biyayya Ga Umarnin Kotu
Manyan Labarai

Natasha Ta Rubuta Wa Majalisa, Tana Neman A Yi Biyayya Ga Umarnin Kotu

2 days ago
Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ
Tsaro

Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ

2 days ago
Next Post

Ka Cire Sarkin Kano Bayero Daga Fadar Nasarawa - Gwamnatin Kano Ga Tinubu

LABARAI MASU NASABA

UTME

An Samu Rarrabuwar Kai Kan Makin Shiga Manyan Makarantu

July 19, 2025
Jami’ar Ilorin Ta Karrama Shugabannin JAMB, THISDAY Da Wasu 63 A Bikin Shekara 50

Jami’ar Ilorin Ta Karrama Shugabannin JAMB, THISDAY Da Wasu 63 A Bikin Shekara 50

July 19, 2025
‘Yansanda Sun Hana Gudanar Da Taron Tunawa Da Ranar Haihuwar Obi A Kaduna

‘Yansanda Sun Hana Gudanar Da Taron Tunawa Da Ranar Haihuwar Obi A Kaduna

July 19, 2025
Abinci

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

July 19, 2025
sallah

Yadda Hauhawar Farashin Kayan Abinci Ya Ragu A Nijeriya

July 19, 2025
Shettima

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

July 19, 2025
Fyade

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

July 19, 2025
APC

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

July 19, 2025
Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.