• English
  • Business News
Friday, September 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yanzu Yanzu – Kotu Ta Soke Zaɓen Ƙananan Hukumomn Ribas

by Abubakar Sulaiman
6 months ago
in Manyan Labarai
0
Yanzu Yanzu – Kotu Ta Soke Zaɓen Ƙananan Hukumomn Ribas
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kotun Ƙoli ta bayyana cewa zaɓen ƙananan hukumomi da aka gudanar a Jihar Rivers a ranar 5 ga Oktoba, 2024, ba shi da inganci, kuma ya saɓa wa doka. Kotun ta yanke hukuncin cewa zaɓen ya kasance haramtacce, kuma saboda rashin bin ƙa’idojin da doka ta tanada kafin gudanar da irin wannan zaɓe.

A cewar kotun, hukumar zabte ta Jihar Rivers (RSIEC) ta karya dokokin gudanar da zabe, inda ta saɓa wa sashi na 150 na dokar zaɓe ta 2022.

A baya dai, wata babbar kotu a Abuja ta hana hukumar zabe ta ƙasa (INEC) bayar da rajistar masu kaɗa ƙuri’a ga RSIEC domin gudanar da zaɓen, bisa hujjar cewa ba a cika sharuɗɗan gudanar da zaɓe ba. Haka kuma, kotun ta hana Sufeto Janar na ‘Yansanda da hukumar tsaro ta DSS samar da tsaro yayin zaɓen, domin gujewa duk wata matsala da ka iya tasowa. Wannan umarni ya biyo bayan ƙarar da jam’iyyar APC ta shigar, tare da rakiyar lauyoyinta Joseph Daudu, Sebastine Hon, da Ogwu James Onoja, dukkaninsu SAN.

  • Shugaban NPA Ya Kai Ziyarar Neman Masu Zuba Jari A Tashoshin Jiragen Ruwa Na Onne Da Ta Jihar Ribas
  • Jam’iyyar APC Ta Sahalewa Shugaba Tinubu Damar Neman Shugabancin Nijeriya A 2027

Kotun ta bayyana cewa RSIEC ta yi kuskure wajen sanya ranar zaɓe ba tare da bin dokokin da suka wajaba ba, ciki har da rashin sanar da jama’a kwanaki 90 kafin a gudanar da zaɓen, kamar yadda doka ta tanada. Haka kuma, an gaza sabunta da tantance rajistar masu kaɗa kuri’a, wanda hakan ya saɓa wa ƙa’idar zaɓe. Saboda haka, kotun ta ayyana cewa zaben bai cika ƙa’idojin doka ba, kuma ba za a amince da sakamakonsa ba.

Bugu da ƙari, kotun ta haramta amfani da rajistar masu kaɗa ƙuri’a da INEC ta tanadar, har sai an cika dukkan sharuddan da doka ta tanada. Wannan hukunci na kotu yana nufin cewa duk wanda aka zaɓa a ƙarƙashin wannan zaɓe ba zai ci gaba da riƙe muƙaminsa ba.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

Tinubu Ya Fara Hutun Aiki Na Kwanaki 10 A Faransa Da Birtaniya

Wannan mataki yana da matuƙar tasiri a siyasar Jihar Ribas, inda jam’iyyar APP ce ta lashe mafi yawan kujeru a zaɓen da aka soke.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ElectionZaɓe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Duk Da Hukuncin Kotun Koli, Har Yanzu Kananan Hukumomi Sun Gaza Samun Cikakken ‘Yanci

Next Post

Ka Cire Sarkin Kano Bayero Daga Fadar Nasarawa – Gwamnatin Kano Ga Tinubu

Related

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

8 hours ago
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Fara Hutun Aiki Na Kwanaki 10 A Faransa Da Birtaniya

13 hours ago
Ibtila’in Ambaliyar Ruwa: Halin Da Birnin Maiduguri Ya Tsinci Kansa A Ciki
Manyan Labarai

Gargaɗi: Ƙauyuka 43 A Jihohi 14 Na Fuskantar Barazanar Ambaliyar Ruwa 

15 hours ago
Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Ƴan Ta’adda 15 A Borno
Manyan Labarai

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Ƴan Ta’adda 15 A Borno

18 hours ago
Tinubu Zai Ƙaddamar Da Masana’antar Battirin Lithium A Nasarawa
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ƙaddamar Da Masana’antar Battirin Lithium A Nasarawa

21 hours ago
Ƴan Siyasar Arewa Na Rigima Da Juna, Tinubu Na Murna — Jibrin
Manyan Labarai

Ƴan Siyasar Arewa Na Rigima Da Juna, Tinubu Na Murna — Jibrin

22 hours ago
Next Post

Ka Cire Sarkin Kano Bayero Daga Fadar Nasarawa - Gwamnatin Kano Ga Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

September 4, 2025
An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

September 4, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

September 4, 2025
Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara

Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara

September 4, 2025
Dakarun PLA Sun Gudanar Da Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin

Dakarun PLA Sun Gudanar Da Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin

September 4, 2025
Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo

Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo

September 4, 2025
Gwamna Sule Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Fara Yaƙin Neman Zaɓe A Nasarawa

Gwamna Sule Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Fara Yaƙin Neman Zaɓe A Nasarawa

September 4, 2025
Xi Ya Gana Da Shugaban Zimbabwe Da Na Jamhuriyar Kongo

Xi Ya Gana Da Shugaban Zimbabwe Da Na Jamhuriyar Kongo

September 4, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Kim Jong Un

Xi Jinping Ya Gana Da Kim Jong Un

September 4, 2025
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

September 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.