ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, June 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yanzu-Yanzu: Wike Ya Jagoranci Tawagar G-5 Don Ganawa Da Gwamnan Bauchi Bayan Sulhunsa Da Atiku

by Sadiq
4 years ago
Wike

Gwamnonin jam’iyyar PDP biyar da aka fi sani da PDP G-5 a karkashin jagorancin gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike, sun yi alkawarin marawa gwamnan Jihar Bauchi Bala Mohammed baya domin samun wa’adi na biyu a zaben badi.

Kungiyar ta bayyana goyon bayan ta ga gwamnan Bauchi a ranar Laraba yayin wata ziyara da suka kai Bauchi domin nuna goyon baya ga gwamna Mohammed.

  • Dan Wasan Senegal Mane Ba Zai Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ba Saboda Rauni 
  • 2023: Atiku da Gwamnan Bauchi Sun Sasanta Rikicin Da Ke Tsakaninsu 

Idan dai za a iya tunawa, gwamnan Jihar Bauchi ya zargi dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar da hada kai da wasu gungun ‘yan siyasa na jihar domin dakile yunkurinsa na sake tsayawa takara a 2023.

ADVERTISEMENT

Sai dai dukkansu sun warware sabanin da ke tsakaninsu tare da yanke shawarar yin aiki tare domin samun nasarar zabe a 2023 bayan wani taro da suka yi a Abuja a daren ranar Talata.

Sai dai da yake magana a madadin Gwamnonin G-5 a gidan Ramat da ke Bauchi, Gwamna Wike ya ce duk abin da ya shafi Gwamna Bala Mohammed shi ma ya shafe su a kungiyance, don haka sun kuduri aniyar goyon bayan takararsa a karo na biyu.

LABARAI MASU NASABA

Kogi: Mambobin APC Sun Koma PDP, Sun Mara Wa Natasha Baya Domin Wa’adi Na Biyu

Ɗan Kwankwaso Ya Zama Mataimakin Ɗan Takarar Gwamnan NDC A Zaɓen Kano na 2027

Ya ce duk da cewa gwamnan Bauchi ya yi kyakkyawan aiki ta yadda al’ummar jihar za su zabe shi a zaben gwamna na 2023, amma suna ganin goyon bayansu a wannan mawuyacin lokaci na da muhimmanci ga gwamnan.

“Ba mu sake tsayawa takara karo na biyu ba duk da cewa wasunmu na neman tikitin ‘yan majalisar dattawa a jihohinsu, ni kadai ne ban tsaya takara ba bayan faduwa zaben fidda gwani na shugaban kasa,” in ji Wike.

Da yake mayar da martani, gwamnan Jihar Bauchi, ya ce goyon bayan da gwamnonin G-5 suke ba shi a wannan lokaci da jam’iyyar ke fuskantar kalubale ya ji dadi.

Sai dai ya yi mamakin dalilin da ya sa ba a mayar da shi cikin tawagar PDP G-5 tun daga farko ba.

“G-5 Gwamnonin sun kore ni ne saboda wasu dalilai da suka fi sanin su. A siyasa sai ku tafi tare da mutanen da kuke da abin da ya kamance da su.” In ji Mohammed.

Gwamnonin G-5 da suka hada da Nyesom Wike, Okezie Ikpeazu na Jihar Abia, Ifeanyi Ugwuanyi na Jihar Enugu da Samuel Ortom na Jihar Benue a halin yanzu suna ganawar sirri da gwamna Mohammed yayin da gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, bai bayyana ba.

LEADERSHIP ta rawaito ganawar ta zo ne a daidai lokacin da aka sasanta tsakanin Gwamna Mohammed da Atiku Abubakar a daren ranar Talata a Abuja.

MASU ALAKA

Kogi: Mambobin APC Sun Koma PDP, Sun Mara Wa Natasha Baya Domin Wa’adi Na Biyu
Siyasa

Kogi: Mambobin APC Sun Koma PDP, Sun Mara Wa Natasha Baya Domin Wa’adi Na Biyu

June 16, 2026
Ɗan Kwankwaso Ya Zama Mataimakin Ɗan Takarar Gwamnan NDC A Zaɓen Kano na 2027
Siyasa

Ɗan Kwankwaso Ya Zama Mataimakin Ɗan Takarar Gwamnan NDC A Zaɓen Kano na 2027

June 15, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki
Labarai

Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

June 14, 2026
Next Post
Ambaliyar Ruwa A Bayelsa: Kiranye-Kirayen Tsige Minista Sadiya Farouq Sam Bai Dace Ba -Gwamnati

Ambaliyar Ruwa A Bayelsa: Kiranye-Kirayen Tsige Minista Sadiya Farouq Sam Bai Dace Ba -Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Na Samar Da Managarcin Yanayi Na Bunkasa Kirkire-kirkire Ga Masana’antun Kasa Da Kasa

Kasar Sin Na Samar Da Managarcin Yanayi Na Bunkasa Kirkire-kirkire Ga Masana’antun Kasa Da Kasa

June 16, 2026
Kogi: Mambobin APC Sun Koma PDP, Sun Mara Wa Natasha Baya Domin Wa’adi Na Biyu

Kogi: Mambobin APC Sun Koma PDP, Sun Mara Wa Natasha Baya Domin Wa’adi Na Biyu

June 16, 2026
Sin Na Goyon Bayan Ci Gaban Manyan Kamfanonin Kasa Da Kasa

Sin Na Goyon Bayan Ci Gaban Manyan Kamfanonin Kasa Da Kasa

June 16, 2026
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Kira Zaman Gaggawa A Ranar 23 Ga Yuni Kan Matsalar Tsaro

June 16, 2026
Sin Ta Bude Kasuwarta Ga Gyadar Sha Zawa Daga Nahiyar Afrika

Sin Ta Bude Kasuwarta Ga Gyadar Sha Zawa Daga Nahiyar Afrika

June 16, 2026
Sojoji Sun Fatattaki Lakurawa, Sun Ƙwato Makamai Da Abubuwan Fashewa A Kebbi

Sojoji Sun Fatattaki Lakurawa, Sun Ƙwato Makamai Da Abubuwan Fashewa A Kebbi

June 16, 2026
Gwamna Radda Ya Ziyarci Matar Janar Rabe Da Aka Ceto, Ya Yaba Wa Sojoji

Gwamna Radda Ya Ziyarci Matar Janar Rabe Da Aka Ceto, Ya Yaba Wa Sojoji

June 16, 2026
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

Peter Obi Ya Nemi A Janye Hukuncin Kotu Kan Soke Rijistar ADC

June 16, 2026
Mataimakin Kwamishinan ‘Yansandan Legas, Khan Salihu, Ya Rasu

Mataimakin Kwamishinan ‘Yansandan Legas, Khan Salihu, Ya Rasu

June 16, 2026
Hauhawar Farashi Ya Kai Kashi 15.93 Cikin 1000 A Watan Mayu A Nijeriya – NBS

Hauhawar Farashi Ya Kai Kashi 15.93 Cikin 1000 A Watan Mayu A Nijeriya – NBS

June 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.