ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yanzu-Yanzu: Wike Ya Jagoranci Tawagar G-5 Don Ganawa Da Gwamnan Bauchi Bayan Sulhunsa Da Atiku

by Sadiq
3 years ago
Wike

Gwamnonin jam’iyyar PDP biyar da aka fi sani da PDP G-5 a karkashin jagorancin gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike, sun yi alkawarin marawa gwamnan Jihar Bauchi Bala Mohammed baya domin samun wa’adi na biyu a zaben badi.

Kungiyar ta bayyana goyon bayan ta ga gwamnan Bauchi a ranar Laraba yayin wata ziyara da suka kai Bauchi domin nuna goyon baya ga gwamna Mohammed.

  • Dan Wasan Senegal Mane Ba Zai Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ba Saboda Rauni 
  • 2023: Atiku da Gwamnan Bauchi Sun Sasanta Rikicin Da Ke Tsakaninsu 

Idan dai za a iya tunawa, gwamnan Jihar Bauchi ya zargi dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar da hada kai da wasu gungun ‘yan siyasa na jihar domin dakile yunkurinsa na sake tsayawa takara a 2023.

ADVERTISEMENT

Sai dai dukkansu sun warware sabanin da ke tsakaninsu tare da yanke shawarar yin aiki tare domin samun nasarar zabe a 2023 bayan wani taro da suka yi a Abuja a daren ranar Talata.

Sai dai da yake magana a madadin Gwamnonin G-5 a gidan Ramat da ke Bauchi, Gwamna Wike ya ce duk abin da ya shafi Gwamna Bala Mohammed shi ma ya shafe su a kungiyance, don haka sun kuduri aniyar goyon bayan takararsa a karo na biyu.

LABARAI MASU NASABA

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

Ya ce duk da cewa gwamnan Bauchi ya yi kyakkyawan aiki ta yadda al’ummar jihar za su zabe shi a zaben gwamna na 2023, amma suna ganin goyon bayansu a wannan mawuyacin lokaci na da muhimmanci ga gwamnan.

“Ba mu sake tsayawa takara karo na biyu ba duk da cewa wasunmu na neman tikitin ‘yan majalisar dattawa a jihohinsu, ni kadai ne ban tsaya takara ba bayan faduwa zaben fidda gwani na shugaban kasa,” in ji Wike.

Da yake mayar da martani, gwamnan Jihar Bauchi, ya ce goyon bayan da gwamnonin G-5 suke ba shi a wannan lokaci da jam’iyyar ke fuskantar kalubale ya ji dadi.

Sai dai ya yi mamakin dalilin da ya sa ba a mayar da shi cikin tawagar PDP G-5 tun daga farko ba.

“G-5 Gwamnonin sun kore ni ne saboda wasu dalilai da suka fi sanin su. A siyasa sai ku tafi tare da mutanen da kuke da abin da ya kamance da su.” In ji Mohammed.

Gwamnonin G-5 da suka hada da Nyesom Wike, Okezie Ikpeazu na Jihar Abia, Ifeanyi Ugwuanyi na Jihar Enugu da Samuel Ortom na Jihar Benue a halin yanzu suna ganawar sirri da gwamna Mohammed yayin da gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, bai bayyana ba.

LEADERSHIP ta rawaito ganawar ta zo ne a daidai lokacin da aka sasanta tsakanin Gwamna Mohammed da Atiku Abubakar a daren ranar Talata a Abuja.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC
Manyan Labarai

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa
Siyasa

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

November 15, 2025
Next Post
Ambaliyar Ruwa A Bayelsa: Kiranye-Kirayen Tsige Minista Sadiya Farouq Sam Bai Dace Ba -Gwamnati

Ambaliyar Ruwa A Bayelsa: Kiranye-Kirayen Tsige Minista Sadiya Farouq Sam Bai Dace Ba -Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

November 17, 2025
Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

November 17, 2025
An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

November 17, 2025
NBS

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

November 17, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

November 17, 2025
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

November 17, 2025
Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

November 17, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

November 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.