• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yanzu-Yanzu: Wike Ya Jagoranci Tawagar G-5 Don Ganawa Da Gwamnan Bauchi Bayan Sulhunsa Da Atiku

by Sadiq
3 years ago
in Siyasa
0
Yanzu-Yanzu: Wike Ya Jagoranci Tawagar G-5 Don Ganawa Da Gwamnan Bauchi Bayan Sulhunsa Da Atiku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnonin jam’iyyar PDP biyar da aka fi sani da PDP G-5 a karkashin jagorancin gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike, sun yi alkawarin marawa gwamnan Jihar Bauchi Bala Mohammed baya domin samun wa’adi na biyu a zaben badi.

Kungiyar ta bayyana goyon bayan ta ga gwamnan Bauchi a ranar Laraba yayin wata ziyara da suka kai Bauchi domin nuna goyon baya ga gwamna Mohammed.

  • Dan Wasan Senegal Mane Ba Zai Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ba Saboda Rauni 
  • 2023: Atiku da Gwamnan Bauchi Sun Sasanta Rikicin Da Ke Tsakaninsu 

Idan dai za a iya tunawa, gwamnan Jihar Bauchi ya zargi dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar da hada kai da wasu gungun ‘yan siyasa na jihar domin dakile yunkurinsa na sake tsayawa takara a 2023.

Sai dai dukkansu sun warware sabanin da ke tsakaninsu tare da yanke shawarar yin aiki tare domin samun nasarar zabe a 2023 bayan wani taro da suka yi a Abuja a daren ranar Talata.

Sai dai da yake magana a madadin Gwamnonin G-5 a gidan Ramat da ke Bauchi, Gwamna Wike ya ce duk abin da ya shafi Gwamna Bala Mohammed shi ma ya shafe su a kungiyance, don haka sun kuduri aniyar goyon bayan takararsa a karo na biyu.

Labarai Masu Nasaba

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

Ya ce duk da cewa gwamnan Bauchi ya yi kyakkyawan aiki ta yadda al’ummar jihar za su zabe shi a zaben gwamna na 2023, amma suna ganin goyon bayansu a wannan mawuyacin lokaci na da muhimmanci ga gwamnan.

“Ba mu sake tsayawa takara karo na biyu ba duk da cewa wasunmu na neman tikitin ‘yan majalisar dattawa a jihohinsu, ni kadai ne ban tsaya takara ba bayan faduwa zaben fidda gwani na shugaban kasa,” in ji Wike.

Da yake mayar da martani, gwamnan Jihar Bauchi, ya ce goyon bayan da gwamnonin G-5 suke ba shi a wannan lokaci da jam’iyyar ke fuskantar kalubale ya ji dadi.

Sai dai ya yi mamakin dalilin da ya sa ba a mayar da shi cikin tawagar PDP G-5 tun daga farko ba.

“G-5 Gwamnonin sun kore ni ne saboda wasu dalilai da suka fi sanin su. A siyasa sai ku tafi tare da mutanen da kuke da abin da ya kamance da su.” In ji Mohammed.

Gwamnonin G-5 da suka hada da Nyesom Wike, Okezie Ikpeazu na Jihar Abia, Ifeanyi Ugwuanyi na Jihar Enugu da Samuel Ortom na Jihar Benue a halin yanzu suna ganawar sirri da gwamna Mohammed yayin da gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, bai bayyana ba.

LEADERSHIP ta rawaito ganawar ta zo ne a daidai lokacin da aka sasanta tsakanin Gwamna Mohammed da Atiku Abubakar a daren ranar Talata a Abuja.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AtikuBala MohammedBauchiPDPSiyasaWike
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dan Wasan Senegal Mane Ba Zai Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ba Saboda Rauni 

Next Post

Ambaliyar Ruwa A Bayelsa: Kiranye-Kirayen Tsige Minista Sadiya Farouq Sam Bai Dace Ba -Gwamnati

Related

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta
Siyasa

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

5 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

8 hours ago
Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson
Siyasa

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

12 hours ago
Gwamnatin APC Ta Kara Ingiza ‘Yan NIjeriya Cikin Bakin Talauci – PDP
Manyan Labarai

PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta

3 days ago
Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC
Manyan Labarai

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

4 days ago
An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027
Siyasa

An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

4 days ago
Next Post
Ambaliyar Ruwa A Bayelsa: Kiranye-Kirayen Tsige Minista Sadiya Farouq Sam Bai Dace Ba -Gwamnati

Ambaliyar Ruwa A Bayelsa: Kiranye-Kirayen Tsige Minista Sadiya Farouq Sam Bai Dace Ba -Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

June 27, 2025
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

June 27, 2025
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

June 27, 2025
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.