• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yanzu-Yanzu: Wike Ya Jagoranci Tawagar G-5 Don Ganawa Da Gwamnan Bauchi Bayan Sulhunsa Da Atiku

by Sadiq
3 years ago
in Siyasa
0
Yanzu-Yanzu: Wike Ya Jagoranci Tawagar G-5 Don Ganawa Da Gwamnan Bauchi Bayan Sulhunsa Da Atiku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnonin jam’iyyar PDP biyar da aka fi sani da PDP G-5 a karkashin jagorancin gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike, sun yi alkawarin marawa gwamnan Jihar Bauchi Bala Mohammed baya domin samun wa’adi na biyu a zaben badi.

Kungiyar ta bayyana goyon bayan ta ga gwamnan Bauchi a ranar Laraba yayin wata ziyara da suka kai Bauchi domin nuna goyon baya ga gwamna Mohammed.

  • Dan Wasan Senegal Mane Ba Zai Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ba Saboda Rauni 
  • 2023: Atiku da Gwamnan Bauchi Sun Sasanta Rikicin Da Ke Tsakaninsu 

Idan dai za a iya tunawa, gwamnan Jihar Bauchi ya zargi dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar da hada kai da wasu gungun ‘yan siyasa na jihar domin dakile yunkurinsa na sake tsayawa takara a 2023.

Sai dai dukkansu sun warware sabanin da ke tsakaninsu tare da yanke shawarar yin aiki tare domin samun nasarar zabe a 2023 bayan wani taro da suka yi a Abuja a daren ranar Talata.

Sai dai da yake magana a madadin Gwamnonin G-5 a gidan Ramat da ke Bauchi, Gwamna Wike ya ce duk abin da ya shafi Gwamna Bala Mohammed shi ma ya shafe su a kungiyance, don haka sun kuduri aniyar goyon bayan takararsa a karo na biyu.

Labarai Masu Nasaba

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Ya ce duk da cewa gwamnan Bauchi ya yi kyakkyawan aiki ta yadda al’ummar jihar za su zabe shi a zaben gwamna na 2023, amma suna ganin goyon bayansu a wannan mawuyacin lokaci na da muhimmanci ga gwamnan.

“Ba mu sake tsayawa takara karo na biyu ba duk da cewa wasunmu na neman tikitin ‘yan majalisar dattawa a jihohinsu, ni kadai ne ban tsaya takara ba bayan faduwa zaben fidda gwani na shugaban kasa,” in ji Wike.

Da yake mayar da martani, gwamnan Jihar Bauchi, ya ce goyon bayan da gwamnonin G-5 suke ba shi a wannan lokaci da jam’iyyar ke fuskantar kalubale ya ji dadi.

Sai dai ya yi mamakin dalilin da ya sa ba a mayar da shi cikin tawagar PDP G-5 tun daga farko ba.

“G-5 Gwamnonin sun kore ni ne saboda wasu dalilai da suka fi sanin su. A siyasa sai ku tafi tare da mutanen da kuke da abin da ya kamance da su.” In ji Mohammed.

Gwamnonin G-5 da suka hada da Nyesom Wike, Okezie Ikpeazu na Jihar Abia, Ifeanyi Ugwuanyi na Jihar Enugu da Samuel Ortom na Jihar Benue a halin yanzu suna ganawar sirri da gwamna Mohammed yayin da gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, bai bayyana ba.

LEADERSHIP ta rawaito ganawar ta zo ne a daidai lokacin da aka sasanta tsakanin Gwamna Mohammed da Atiku Abubakar a daren ranar Talata a Abuja.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AtikuBala MohammedBauchiPDPSiyasaWike
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dan Wasan Senegal Mane Ba Zai Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ba Saboda Rauni 

Next Post

Ambaliyar Ruwa A Bayelsa: Kiranye-Kirayen Tsige Minista Sadiya Farouq Sam Bai Dace Ba -Gwamnati

Related

Labarai

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

9 hours ago
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC
Labarai

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

13 hours ago
Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 
Siyasa

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

3 days ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

4 days ago
Hoton Kwankwaso da Ganduje da Shekarau
Bakon Marubuci

Daga Sawaba Zuwa Asara: Baje Kolin Kasuwancin Siyasa A Kano – Auwalu Anwar

5 days ago
Na Yafe Wa Buhari Duk Abin Da Ya Min – Buba Galadima
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ci Amanar Kano, Babu Batun Haɗin Guiwa Tsakaninsa Da Kwankwaso A 2027 – Galadima

6 days ago
Next Post
Ambaliyar Ruwa A Bayelsa: Kiranye-Kirayen Tsige Minista Sadiya Farouq Sam Bai Dace Ba -Gwamnati

Ambaliyar Ruwa A Bayelsa: Kiranye-Kirayen Tsige Minista Sadiya Farouq Sam Bai Dace Ba -Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

August 25, 2025

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.