ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Atiku da Gwamnan Bauchi Sun Sasanta Rikicin Da Ke Tsakaninsu 

by Sadiq
4 years ago
Atiku

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar, da gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, sun sasanta rikicin da ke tsakaninsu, tare da kudurin yin aiki tare domin samun nasarar zabe a babban zaben badi. 

A baya LEADERSHIP ta rawaito cewa Gwamna Mohammed, ya ce ba zai yi kasa a gwiwa ba wajen ficewa daga kwamitin yakin neman zaben jam’iyyar PDP na shugaban kasa idan har dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar ya gaza fitowa fili ya karyata wadanda ke yi masa aiki tare da bayyana goyon bayansa na sake tsayawa takara a karo na biyu a Jihar Bauchi.

  • 2023: Gwamnan Akwa Ibom Ya Karyata Ajiye Mukaminsa Na Shugaban Yakin Zaben Atiku Da Okowa
  • Yin Amfani Da Yanar Gizo Wajen Raya Duniya

Mohammed, wanda shi ne mataimakin shugaban jam’iyyar a Arewa, ya bayyana haka a wata wasika mai shafi takwas da ya aike wa shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Sanata Dr. Iyiocha Ayu.

ADVERTISEMENT

Ayu da wasu jiga-jigan jam’iyyar sun yi gaggawar kai wa gwamnan Jihar Bauchi ziyara a kwanakin baya.

Duk da cewa taron a sirri aka yi, shugabannin jam’iyyar sun yi watsi da duk wani ra’ayi na sabon rikici a tsakaninsu.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

A ci gaba da taron na Bauchi Atiku ya kuma yi wata ganawa da Gwamna Mohammed da wasu masu ruwa da tsaki na jam’iyyar a Abuja a daren ranar Talata.

Da yake bayyana sakamakon taron Abuja da aka yi a safiyar ranar Laraba ta shafinsa na Facebook da aka tabbatar, Atiku ya rubuta cewa: “A daren jiya na karbi bakuncin wasu daga cikin jiga-jigan jam’iyyarmu ta PDP a Abuja, mun tattauna halin da jam’iyyarmu da al’ummar kasar nan ke ciki, kuma muka sake komawa kan lamarin don aikin kishin kasa don murmurewa da dawo da Nijeriya don dawo kasa turbar daidai. – AA.”

Idan dai ba a manta ba PDP ta yi ta fafatawa da kungiyar gwamnoni biyar (PDP G5) wato gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Ezenwo Wike da takwarorinsa na Abia, Oyo, Enugu da Jihar Benue, Okezie Ikpeazu, Seyi Makinde, Ifeanyi Ugwuanyi. da Samuel Ortom.

A baya-bayan nan dai sun kara zafafa adawa da yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar.

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Dan Wasan Senegal Mane Ba Zai Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ba Saboda Rauni 

Dan Wasan Senegal Mane Ba Zai Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ba Saboda Rauni 

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.