• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yara 160,000 Ke Rayuwa Da Cutar Ƙanjamau A Nijeriya —NACA

by Idris Aliyu Daudawa
10 months ago
in Labarai
0
Yara 160,000 Ke Rayuwa Da Cutar Ƙanjamau A Nijeriya —NACA
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugabar hukumar hana yaduwar cutar kanjamo ta kasa (NACA) DoktaTemitope Ilori, ta ce har yanzu lamarin kokarin da ake  yi na hana da, ya dauki cutar daga wurin uwa, da kuma yara wadanda suke dauke da cutar har yanzu abin ya tsaya ne a kashi 33, wato bai kai ga kashi 95 da ake son cimmawa ba.

Da take jawabi da kuma tunawa da rahoton UNAIDS na shekarar 2023, Dokta Ilori ta ce ku san yara 160,000  da suke 0-14 suna rayuwa ne da cutar kan jamo a Nijeriya.

  • Tashin Farashin Kayan Masarufi Ya Fi Illa Ga Mazauna Jihohin Sakkwato, Edo Da Borno
  • Dalilan Da Suka Jefa ‘Yan Nijeriya Cikin Talauci Duk Da Karuwar Kudin Shiga – Masana

Shugabar ta bayyana hakan ne ranar Litinin a Abuja lokacin taron manema labarai kafin ranar cutar kanjamo ta shekarar 2024, mai taken: “A dauki hanyar da ta dace:  Ci gaba da amfani da maganin da ya dace, hana yaduwar cutar HIB tsakanin yara, saboda a kawo karshen cutar nan da shekarar ta 2030”.

Bikin ranar kanjamo ana yin shi ne kowace shekara 1 ga watan Disamba domin a samu wayar da kan al’umma dangane da cutar da kuma kwayar cutar da take sanadiyar ta.

A kan yadda cutar take har ila yau shugabar tace mutane milyan 1.4 ne masu shekaru daga 15 zuwa 64 da akwai mutane milyan biyu da suke rayuwa da cutar a Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

Bugu da kari kuma an samu mutane 22,000 da suka kamu da sabuwar cutar HIB sai kuma mutuwar mutane 15,000 a ko wace shekara.

“Nijeriya na da mutane da suka kai kashi 1.4 cikin 100, daga cikin al’ummarta masu shekaru daga,15 zuwa 64 da suka kai milyan 2 da suke rayuwa da cutar HIB.

“Kasar tana ci gaba da fuskantar matsala dangane da yadda ake kamuwa da cutar ko yadda ta ke shiga daga uwa zuwa danta tun yana cikin mahaifa. Rahoton UNAIDS na 2023 ya nuna kusan yara 160,000 da shekarunsu daga  0-14 ke rayuwa da cutar HIB, yayin da aka samu mutane 22,000 da suka kamu da cutar sai kuma  mutum 15,000 da suke mutuwa duk shekara,a  sanadiyar cutar kamar yadda ta yi bayani.

Sai dai kuma duk da hakan tace ma’aikatar lafiya ta tarayya da walwalar jama’a, kamar yadda Dokta Ilori ta bayyana  bada dadewa bane ta kafa wani kwamitin kasa wanda zai domin ya tabbatar da ana aiwatar da abinda aka yi niyyar yi.

Ta kara jaddada NACA ta kaddamar da kwamiti a Jihohi uku inda ta fara magana kai tsaye da gwamnoni uku su bada taimako  kaddamarwar da za’ayi, da kuma samar da wani kwamiti kamar  shi  a zaman na bangaren Jiha,da niyyar tabbatar da ba wani jaririn da za’a sake haifa dauke da cutar HIB  a Nijeriya.

“Wannan abin haka zai kasance a Jihohi 36 da babban birnin tarayya bada dadewa ba ,”  ta kara jaddada shirin hukumar dake yi ma jagoranci da zata ci gaba duk wasu tsare- tsaren taimakawa kawo karshen cutar kanjamo, koda kuwa ace su masu taimakawar za su nuna gazawa ko su bari.

“Tawaga ta, ta dade tana ganawa da masu ruwa da tsaki kan lamarin HIB wajen taimakawar da suke yi, inda har ma suna samar da wani hali na yiyuwar ci gaba dayin hakan domin kada a bari a tafka asarar nasarar da aka fara samu.Daga nan kum a samu damar sa gwamnatcin Jihohi a cikin lamarin inda ita ma za ta bada nata taimakon wajen samar da duk abubuwan da ake bukata lokacin aiwatar da tsarin a Jihohi.

“Manufar wannan dabarar kamar yadda ta yi karin bayani koda ace su masu taimakawa sun daina, babu wani abinda zai tada hankalin kasa, idan dai ana maganar matakan hana yaduwa da kawo karshen cutar HIB, har ma da wasu cututtukan da suke da alaka da ita.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Karancin Takardar Kudi: Masu POS Da Bankuna Na Wasa Da Hankulan Jama’a

Next Post

Yunkurin ACF Na Mara Wa Dan Takarar Arewa Baya A 2027 : Ta Ina Za A Fara?

Related

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi
Labarai

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

48 minutes ago
Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya
Labarai

Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

2 hours ago
Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana
Labarai

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

10 hours ago
Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki
Labarai

Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

11 hours ago
Shettima
Labarai

Shettima Ya Bada Umarnin Gaggauta Raba Lamunin Naira Biliyan 250 Ga Ƙananan Manoma 

12 hours ago
Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 
Labarai

Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

13 hours ago
Next Post
Yunkurin ACF Na Mara Wa Dan Takarar Arewa Baya A 2027 : Ta Ina Za A Fara?

Yunkurin ACF Na Mara Wa Dan Takarar Arewa Baya A 2027 : Ta Ina Za A Fara?

LABARAI MASU NASABA

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

September 12, 2025
Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

September 12, 2025
Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

September 12, 2025
Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

September 12, 2025
Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

September 11, 2025
Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

September 11, 2025
Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

September 11, 2025
Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

September 11, 2025
Shettima

Shettima Ya Bada Umarnin Gaggauta Raba Lamunin Naira Biliyan 250 Ga Ƙananan Manoma 

September 11, 2025
An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.