• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yau Alhamis Za A Yanke Hukunci Kan Malamin Da Ake Zargi Da Yi Wa Dalibarsa Kisan Gilla A Kano

by Muhammad
3 years ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Yau Alhamis Za A Yanke Hukunci Kan Malamin Da Ake Zargi Da Yi Wa Dalibarsa Kisan Gilla A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Alhamis dinnan ne ake sa ran wata babbar kotun jihar Kano za ta yanke hukunci kan kisan da aka yi wa karamar yarinyar nan, Hanifa Abubakar.

BBC ta wallafa a shafinta cewa, ana zargin malaminta Abdulmalik Tanko ne ya sace ta a watan Dasambar 2021 tare da kashe yarinyar mai shekara biyar, kana ya binne gawarta a gidansa.

  • Kotu Ta Saka Ranar Yanke Hukunci Akan Wanda Ake Zargi Da Kashe Hanifa
  • Jami’an KAROTA Sun Damke Bakin Haure Dauke Da Muggan Makamai A Kano

Kisan nata ya ja hankalin duniya inda dubban mutane, ciki har da shugaban Nijeriya, Muhammadu Buhari, suka yi tur da shi.

Bayanai sun tabbatar da cewa wasu mutane ne suka ɗauke ta a babur mai kafa uku da ake kira A-Daidaita-Sahu bayan ta dawo daga makaranta a kan hanyarta ta zuwa gida inda suka tafi da ita.

An yi ta nema da cigiya amma sai bayan kwana 46 aka ji ɗuriyarta.

Labarai Masu Nasaba

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

A watan Janairu ne aka gano gawar yarinyar da aka sace a ranar 4 ga watan Disambar 2021.

‘Yanda sanda sun tono gawarta tata wadda ake zargi Abdulmalik Tanko, mai makarantar Noble Kids Academy, ya binne a wani rami.

An zarge shi da hada baki da Isyaku Hashim da matarsa Fatima Jibril da laifukan da suka hada da hada baki wajen aikata laifi, da satar mutum da kuma tsare yarinyar da suka sace ba tare da amincewarta ba da kuma kisan kai.

Sai dai kotu ta bayar da umarnin sakin Fatima Jibril bayan ta yi nasarar wanke kanta daga zarge-zargen a gaban kotu.

An kwashe kimanin watanni shida ana shari’ar wadda Mai Shari’a Sulaiman Na’abba yake jagoranta.

Tun lokacin da lamarin ya faru ne aka ƙaddamar da binciken hadin gwiwa tsakanin jami’an tsaro na farin kaya na DSS da ƴan sanda da jami’an Civil Defence. Mai magana da yawun rundunar ƴan sanda jihar Kano ya shaida wa manema labarai a ranar da aka gano gawar tata cewa jim kaɗan bayan sace Hanifa sai ɓarayin suka kira iyayenta suna neman kuɗin fansa har kimanin naira miliyan shida.

Bayan samun rahoton ne sai Kwamishinan ƴan sanda na jihar ya haɗa taron gaggawa na manyan shugabannin tsaro don gano cewa an gano ƙarin dabarun tabbatar da tsaro a jihar Kano.

Daga nan kuma sai rundunar ƴan sanda ta tayar da tawagar ‘Kan Ka ce Kwabo’, wato Operation Puff Ader don tabbatar da kamo waɗanda suka sace yarinyar.

“Da aka ci gaba da bibiya aka yi ta aiki da har nasara ta kai aka kama mutum biyu da farko, wato Abdulmalik Muhammad Tanko mai shekara 30 da abokinsa Hashim Isiyaku mai shekara 37 da suke unguwar Tudun Murtala, kuma jami’an DSS suka yi nasarar kama su,” in ji DSP Abdullahi Haruna Kiyawa.

“Daga binciken da aka fara ne Abdulmalik ya tabbatar da cewa Hanifa dalibarsa ce tana karatu a makarantar da yake koyarwa a Kwanar Dakata. Ya sace ta ne ya kai ta gidansa ya ɓoye ta har kimanin sati biyu, ya kuma nemi a ba shi kuɗi har naira miliyan shida.

“Ranar 18 ga watan 12 da ya fahimci ana so a gano cewa yarinyar tana tare da shi, don har gidansa ana ta bibiya an je, sai ya gaya mana (ƴan sanda) cewa ya ba ta guba ta sha ta mutu.

“Daga nan sai suka haɗa baki da wancan abokin nasa Hashim suka ɗauke ta suka sa a buhu suka kai ta wannan makarantar suka yi tono suka binne ta,” kamar yadda kakakin ƴan sanda ya ce.

DSP Kiyawa ya ƙara da cewa “sai a yau 20 ga watan Janairun 2021 ne muka yi nasarar kamo su.”

Kakakin ƴan sanda ya ce sun fara da yi wa Hashim tambayoyi ne inda ya tabbatar da cewa haƙiƙa Abdulmalik ya neme shi ya taya shi wani aiki cewa akwai abin da za su je su binne a buhu, kuma ya taimaka masa wajen yin tonon a cikin makarantar suka kuma binne.

Sannan ya gaya wa ƴan sanda cewa kafin ma wannan lokacin shi Abdulmalik din ya samu Hamshim shi da wata Fatima Jibrin Musa mai shekara 27 da ke zaune a Tudun Murtala, ya kuma ce musu su je su sato masa wannan yarinya, amma sun ce daga baya sun gaya masa ba za su yi ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda ’Yan Kasuwa Suka Rufe Kasuwanni A Legas Don Yankar Katin Zabe

Next Post

Buhari Ya Gaji, Ya Kamata Ya Koma Gida Ya Huta Kawai – Elumelu

Related

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina
Kotu Da Ɗansanda

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina

3 days ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

3 weeks ago
Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa
Kotu Da Ɗansanda

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

3 weeks ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

4 weeks ago
‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

2 months ago
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe
Kotu Da Ɗansanda

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

2 months ago
Next Post
Jerin Sunayen Sabbin Ministocin Da Buhari Ya Aike Wa Majalisar Dattijai Ta Tantance Su

Buhari Ya Gaji, Ya Kamata Ya Koma Gida Ya Huta Kawai – Elumelu

LABARAI MASU NASABA

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

August 3, 2025
Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

August 3, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

August 3, 2025
Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC

Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC

August 3, 2025
Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

August 2, 2025
Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

August 2, 2025
Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

August 2, 2025
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

August 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.