ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’an KAROTA Sun Damke Bakin Haure Dauke Da Muggan Makamai A Kano

by Sadiq
4 years ago
KAROTA

Hukumar Kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa ta Jihar Kano (KAROTA), ta ce jami’anta sun damke wasu matasa da ake zargin bata-gari ne dauke muggan makamai a karkashin gadar Dangi da ke jihar.

KAROTA ta bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da kakakinta, Nabilusi Abubakar Kofar Na’isa, ya raba wa manema labarai a yau Talata.

  • Buhari Ya Bukaci Majalisa Ta Amince Da Nadin Ariwoola A Matsayin Alkalin Alkalai Na Kasa
  • ‘Yan Bindiga Sun Kutsa Cikin Gidaje Da Dama A Kaduna, Suna Sace Jama’a

Sanarwar ta ce, jami’an sintiri na hukumar ne suka samu nasarar cafke matasan da daddare a karkashin gadar Dangi.

ADVERTISEMENT

Haka kuma hukumar ta ce, guda daga cikin jami’anta da suka cafke wadanda ake zargin, mai suna Mas’ud Ya’u Yusuf ya ce, sun kama su ne lokacin da suka iske su suna kwance a karkashin gadar, inda suka same su da nau’ikan kayan shaye-shaye da makamai.

Sanarwar ta kara da cewa wadanda ake zargin sun fada wa hukumar cewa kwanansu hudu da shigowa garin Kano daga jihohin Katsina da Zamfara.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Hukumar ta ce, bayan kammala bincike ta mika matasan ga rundunar ‘yan sandan don fadada bincike tare da daukar mataki na gaba.

Shugaban hukumar, Baffa Babba Dan’agundi ya yaba da kokarin jami’an, sannan ya yi kira ga daukacin al’ummar jihar da su ci gaba da kai rahoton duk wani motsi na wadansu mutane da ba su yarda da su ba domin tabbatar da tsaron unguwanni da ma jihar Kano baki daya.

MASU ALAKA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
Labarai

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Next Post
Tirelar Kwasar Shara Ta Hallaka Sojoji 2 A Kaduna

Tirelar Kwasar Shara Ta Hallaka Sojoji 2 A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.