• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaushe Kasashen Yamma Za Su Iya Daukar Nauyin Da Ke Bisa Wuyansu

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Yaushe Kasashen Yamma Za Su Iya Daukar Nauyin Da Ke Bisa Wuyansu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanan baya, an gudanar da taron kolin kasashen Afirka game da daidaita matsalar sauyin yanayi a birnin Rotterdam na kasar Netherlands, inda shugabannin kasashen Afirka guda shida suka hallara, a yayin da firaministan kasar Netherland shi kadai ya halarci taron, ba tare da shugabannin sauran kasashen yamma da aka ba su goron gayyata ba, ciki har da Faransa da Norway da Canada da sauransu.

Hakan ya bakanta ran shugabannin kasashen Afirka. Shugaban kasar Senegal Macky Sall, wanda kuma shi ne shugaban karba karba na kungiyar tarayyar Afirka, ya furta a wajen bikin bude taron cewa, “Abin bakin ciki shi ne, na lura da rashin hallarar shugabannin kasashe masu ci gaban masana’antu a wajen taron.

  • Sin Da Afirka Sun Zamo Manyan Abokan Tafiya A Tafarkin Wanzar Da Ci Gaba

Na yi zaton idan mun yi kokari mun bar Afirka har mun zo Rotterdam, to, mutanen kasashen Turai da sauransu za su fi samun saukin halartar taron.” Shugaban jamhuriyar dimokuradiyyar Congo, Félix-Antoine Tshisekedi Tshilombo, shi ma ya yi suka cewa, “Sanin kowa ne su ne suka fi lalata yanayin duniyarmu.”

Abun hakan yake, kafin kasashe masu tasowa suka fara raya masana’antu, tuni masana’antun kasashe masu sukuni na yammacin duniya suka fara fitar da iska mai gurbata muhalli a shekaru kusan 200 da suka wuce.

Dan tasiri kadan ne kasashen Afirka, da ma sauran kasashe masu tasowa suka haifar ga sauyin yanayin duniya, amma illolin da sauyin yanayin ke haddasawa sun fi addabarsu.

Labarai Masu Nasaba

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

A sabo da haka, kasashen duniya sun cimma yarjejeniyar sauyin yanayi ta MDD da ma yarjejeniyar Paris, wadanda suka bukaci kasashe masu ci gaba su dauki matakai na kayyade iskar Carbon da suke fitarwa, tare kuma da samar da kudade da ma fasahohi ga kasashe masu tasowa wajen daidaita matsalar. Sai dai abin takaici shi ne, ba a aiwatar da yarjejeniyoyin yadda ya kamata ba, kuma kasashen Turai da Amurka ma sun gaza cika alkawuransu, na taimakawa kasashe masu tasowa wajen tinkarar sauyin yanayi.

Rashin hallarar shugabannin kasashen yamma a wajen taron, ya shaida yadda suke rashin girmama kasashen Afirka a kullum, baya ga kuma yadda suke gudun daukar nauyin da ke bisa wuyansu. Ba kawai sauyin yanayi na shafar makomar kasashen Afirka ba ne, har ma yana shafar makomar bai daya ta ‘yan Adam da ta duniyarmu baki daya.

Kamar dai yadda Amina Mohammed, mataimakiyar babban sakataren MDD ta bayyana a wajen taron, “da fika-fikai biyu ne tsuntsu ke iya tashi”, dole ne kasashen Yamma su gane cewa, makomar dan Adam daya ce, kuma su cika alkawuran da suka dauka, tare da daukar nauyin da ke bisa wuyansu, ta fannin daidaita matsalar sauyin yanayi.”(Mai Zane:Mustapha Bulama)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yarima Bin Salman Ba Zai Halarci Jana’izar Sarauniyar Ingila Ba

Next Post

Biyayya Ga Umarnin Allah Ne Kadai Zai Kawo Karshen Matsalolin Nijeriya —Sheikh Yusuf Ali

Related

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

3 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

4 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

5 hours ago
Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

17 hours ago
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

21 hours ago
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

22 hours ago
Next Post
Biyayya Ga Umarnin Allah Ne Kadai Zai Kawo Karshen Matsalolin Nijeriya —Sheikh Yusuf Ali

Biyayya Ga Umarnin Allah Ne Kadai Zai Kawo Karshen Matsalolin Nijeriya —Sheikh Yusuf Ali

LABARAI MASU NASABA

Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.