• English
  • Business News
Sunday, July 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Da Afirka Sun Zamo Manyan Abokan Tafiya A Tafarkin Wanzar Da Ci Gaba

by Leadership Hausa
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Sin Da Afirka Sun Zamo Manyan Abokan Tafiya A Tafarkin Wanzar Da Ci Gaba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ga duk mai waiwayar yanayi da duniya ke ciki a shekarun baya bayan nan, ya kwana da sanin yadda kalubale daban daban ke addabar sassan kasa da kasa.

Duniya ta jima ba ta fuskanci matsi makamancin wanda ake gani a halin yanzu ba, kana daga barkewar annobar COBID-19, zuwa tabarbarewar tattalin arzikin kasashe da dama, mai nasaba da tasirin yaduwar cutar, zuwa matsalar makamashi, da hatsi da takin zamani, wadanda suka biyo bayan barkewar rikicin kasashen Rasha da Ukraine.

  • Kasar Sin Ta Sake Bayyana Matsayinta Kan Rahoton Ofishin OHCHR Dangane Da Jihar Xinjiang
  • Malam Ina So A Taimaka Mun Da Maganin Damuwa Da Bakin Ciki?

A yanzu kuma, cutar gyandar biri na kara bazuwa a wasu sassan duniya, wadda ita ma masana ke cewa, tana bukatar matakan gaggawa na shawo kan ta, kafin ta zamewa duniya alakakai.

Masana da dama sun sha bayyana cewa, idan har ana fatan shawo kan wadannan kalubale, da ma makamantansu da duniya ka iya fuskanta a nan gaba, ya zama wajibi sassan kasa da kasa su yi hadin gwiwa da juna, su hada karfi da karfi, bisa manufar “Gudu tare a tsira tare”.

Hakan ne kuma ya sanya a baya bayan nan, muke ganin yadda kasashen nahiyar Afirka ke ta karbar bakuncin manyan jami’ai daga sassan Turai da Amurka, wadanda ke ziyartar nahiyar da nufin karfafa alakar kasashen su da kasashen na Afirka, a wani mataki na fadada damammakin wanzar da hadin gwiwa don bunkasa ci gaba tare.

Labarai Masu Nasaba

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

To sai dai kuma Bahaushe kan ce, “Wanda ya riga ka bicci dole ya riga ka tashi”.

Tuni kasashen Afirka suka jima da kulla kyakkyawar alakar sada zumunta da kasar Sin, da cudanyar al’adu, da amince ta fuskar siyasa, da kafa ginshiki mai karfi na samar da muhimman ababen more rayuwa, karkashin shawarar nan ta “Ziri daya da hanya daya” wadda kasar ta Sin ta gabatarwa duniya.

Abokan Tafiya

Kaza lika dandalin raya hadin gwiwa na Sin da kasashen Afirka ko FOCAC a takaice, na daf da cika shekaru 22 da kafuwa, wanda karkashinsa, kasar Sin ke ingiza ci gaban Afirka daga dukkanin fannoni.

A watan Nuwambar bara, bisa kwazon sassan biyu, an yi nasarar gudanar da taron ministoci karo na takwas na dandalin FOCAC a birnin Dakar na kasar Senegal.

Har ma a yayin taron aka amince da kudurori guda hudu, ciki har da sanarwar Dakar.

Kaza lika yayin taron na Dakar, shugaban kasar Sin Di Jinping, ya bayyana kaddamar da shirye-shirye guda tara, da nufin bunkasa hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka.

Makasudin wadannan shirye-shirye kuwa shi ne karfafa kawancen gargajiya, da kara inganta abokantaka, da hadin kai, da gina al’umma mai kyakkyawar makomar bai daya tsakanin Sin da kasashen Afirka a sabon zamani da ake ciki.

A nata bangare, nahiyar Afirka ta yi tsayuwar daka wajen goyon bayan kasar Sin a dukkanin lokuta a tarihi. Kasashen nahiyar sun amince da manufar “kasar Sin daya tak a duniya”, suna marawa Sin baya, a kokarinta na kare ikon mulkin kai da tsaron yankunanta.

Kaza lika sassan biyu suna tunkarar kalubalen rayuwa a matakin kasa da kasa da na shiyyoyinsu tare.

Tuni dai “Kwalliya ta fara biyan kudin sabulu”, domin kuwa nasarorin da Sin tare da kasashen Afirka ke samu, sun zamo wani ginshiki na kare muradu, da moriyar kasashe masu tasowa.

Sun kuma rungumi dokoki da ka’idojin majalissar dinkin duniya, inda suke yayata muhimmancin cudanyar dukkanin sassa cikin adalci.

A bangaren samar da manyan ababen more rayuwa da Sin ke tallafawa wajen gina su a nahiyar Afirka, an kai ga kammala babbar gadar Foundiougne ta kasar Senegal, da layin dogo na jiragen kasa dake hada birnin Nairobi zuwa Mumbasa, da babbar hanyar mota ta zamani dake birnin Nairobi, da makamanciyarta da ta tashi daga Kribi zuwa Lolabe a kasar Kamaru.

Kana an kaddamar da layin dogo na sufurin jiragen kasa mai aiki da lantarki, wanda aka yiwa lakabi da “10th of Ramadan” a kasar Masar.

Abokan Tafiya

Dukkanin wadannan ayyuka bangare ne na bunkasa ikon kasashen Afirka, na inganta ci gaban tattalin arziki, masana’antu, da jin dadin jama’a.

Kasar Sin ta fara cika manyan alkawura da ta dauka, tun bayan wancan taron na Dakar, duk da manyan kalubale da duniya ke ciki.

Karkashin hakan, ta samar da lamuni na sama da dalar Amurka biliyan uku, cikin jimillar dala biliyan 10 da ta alkawarta bayarwa ga cibiyoyin hada hadar kudade dake nahiyar, yayin da ta samar da karin kudaden rance har dala biliyan 2.5, domin gudanar da muhimman ayyukan raya kasa a wasu kasashen na nahiya.

Kaza Sin ta shigar da kudade da yawansu ya haura dala biliyan biyu, cikin jimillar dala biliyan 10, a fannin hada hadar cinikayya tsakaninta da Afirka.

A daya bangaren kuma, kamfanonin kasar Sin sun zuba jarin da ya kai dala biliyan 2.17 a sassan kasashen Afirka.

Abokan Tafiya

Hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka, ya haifar da gagarumar nasara a fannin dakile kamfar abinci.

A shekarar nan ta 2022 kadai, Sin ta sanya hannu kan yarjejeniyoyin kawar da biyan harajin kwastam tsakaninta da kasashen Afirka 12 kan wasu hajoji da suka kai kaso 98 bisa dari, cikin jimillar hajojin da kasashen ke shigarwa cikin kasar Sin.

Kasashen Djibouti, da Habasha, da Somalia, da Eritrea sun samu tallafin hatsi kai tsaye daga kasar Sin.

Yayin da karin kasashen Afirka ke samun damar shigar da albarkatun gona zuwa Sin.

Abokan Tafiya

Karkashin ayyukan kiwon lafiya kuwa, sassan biyu sun gudanar da ayyukan yaki da cutar COBID-19 yadda ya kamata.

Sin ta samar da alluran rigakafin COBID-19 miliyan 189 ga kasashen Afirka 27.

A gefe guda, bisa hadin gwiwar Sin da Afirka, nahiyar Afirka ta kai ga fara sarrafa rigakafin COBID-19, wanda yawansa zai kai kimanin miliyan 400 a duk shekara.

Bugu da kari, ana sa ran kammala ginin helkwatar yaki da cututtuka ta Afirka ko “Africa CDC”, nan gaba cikin shekara mai zuwa.

Wannan kari ne kan cibiyoyi da asibitocin sada zumunta na Sin da Afirka dake kasashe irin su Guinea, da Sudan ta kudu, da jamhuriyar Afirka ta tsakiya, da Chadi, da Malawi.

Abokan Tafiya

Masharhanta na ganin ko shakka babu, hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka na da kyakkyawar makoma.

Abun da ake bukata kawai shi ne sassan biyu su rike gaskiya, da amincewar juna.

Su ci gaba da goyon baya, da tallafawa juna kamar yadda suka saba.

Batun tabbatar da ’yancin dukkanin sassan biyu, na ikon mulkin kai da tsaron yankunansu, da wanzar da zaman lafiya da lumana na da matukar muhimmanci ga dorewar nasarorin da suke samu a yanzu.

Don haka kasar Sin ta alkawarta ci gaba da tallafawa kasashen Afirka, ta yadda za su iya warware matsalolinsu da kansu.

Ta kuma sha jaddada manufarta, ta kauracewa tsoma baki cikin harkokin gidan kasashen na Afirka, kamar dai yadda hakan ke kunshe cikin ka’idojin cudanyar kasa da kasa, na akidun majalissar dinkin duniya.

Yayin da Sin da kasashen Afirka ke kan turba ta samun ci gaba tare, ya zama wajibi su zurfafa kawance, da fadada cudanya tsakanin al’ummun su.

Kaza lika yana da kyau, su kara budewa juna kofofin cudanyar al’adu da cinikayya, da cimma moriyar juna a al’amuran duniya baki daya, da ma na shiyyoyi.

A sabon yanayin duniya na yanzu, alamu sun nuna cewa, Sin za ta ci gaba da aiki tare da kasashen Afirka, wajen karfafa ayyukan da aka tsara, karkashin dandalin FOCAC, ta yadda zai zamo silar kara kyautata dangantakar sassan biyu.

Bahaushe kan ce “Da abokin daka a kan sha gari”, ko shakka babu, al’ummun Sin da na kasashen nahiyar Afirka, za su jima suna girbar yabanyar da aka dasa a yanzu, cikin yalwa da aminci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ci GabaHabaka ArzikiNijeriyaSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

A Ceto Kwalejin Kimiyya Da Fasaha Ta Nuhu Bamalli –Kungiyar Malamai

Next Post

Atiku Ya Gana Da ‘Ƴan Takarar Gwamna Na Jam’iyyar PDP

Related

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC
Manyan Labarai

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

7 hours ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

14 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

18 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

1 day ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

2 days ago
Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace
Manyan Labarai

Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace

2 days ago
Next Post
Atiku Ya Gana Da ‘Ƴan Takarar Gwamna Na Jam’iyyar PDP

Atiku Ya Gana Da 'Ƴan Takarar Gwamna Na Jam'iyyar PDP

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

July 5, 2025
Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

July 5, 2025
‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

July 5, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

July 5, 2025
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

July 5, 2025
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

July 5, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

July 5, 2025
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

July 5, 2025
Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.