ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaushe Kasashen Yamma Za Su Iya Daukar Nauyin Da Ke Bisa Wuyansu

by CMG Hausa
4 years ago
Kasashen yamma

Kwanan baya, an gudanar da taron kolin kasashen Afirka game da daidaita matsalar sauyin yanayi a birnin Rotterdam na kasar Netherlands, inda shugabannin kasashen Afirka guda shida suka hallara, a yayin da firaministan kasar Netherland shi kadai ya halarci taron, ba tare da shugabannin sauran kasashen yamma da aka ba su goron gayyata ba, ciki har da Faransa da Norway da Canada da sauransu.

Hakan ya bakanta ran shugabannin kasashen Afirka. Shugaban kasar Senegal Macky Sall, wanda kuma shi ne shugaban karba karba na kungiyar tarayyar Afirka, ya furta a wajen bikin bude taron cewa, “Abin bakin ciki shi ne, na lura da rashin hallarar shugabannin kasashe masu ci gaban masana’antu a wajen taron.

  • Sin Da Afirka Sun Zamo Manyan Abokan Tafiya A Tafarkin Wanzar Da Ci Gaba

Na yi zaton idan mun yi kokari mun bar Afirka har mun zo Rotterdam, to, mutanen kasashen Turai da sauransu za su fi samun saukin halartar taron.” Shugaban jamhuriyar dimokuradiyyar Congo, Félix-Antoine Tshisekedi Tshilombo, shi ma ya yi suka cewa, “Sanin kowa ne su ne suka fi lalata yanayin duniyarmu.”

ADVERTISEMENT

Abun hakan yake, kafin kasashe masu tasowa suka fara raya masana’antu, tuni masana’antun kasashe masu sukuni na yammacin duniya suka fara fitar da iska mai gurbata muhalli a shekaru kusan 200 da suka wuce.

Dan tasiri kadan ne kasashen Afirka, da ma sauran kasashe masu tasowa suka haifar ga sauyin yanayin duniya, amma illolin da sauyin yanayin ke haddasawa sun fi addabarsu.

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

A sabo da haka, kasashen duniya sun cimma yarjejeniyar sauyin yanayi ta MDD da ma yarjejeniyar Paris, wadanda suka bukaci kasashe masu ci gaba su dauki matakai na kayyade iskar Carbon da suke fitarwa, tare kuma da samar da kudade da ma fasahohi ga kasashe masu tasowa wajen daidaita matsalar. Sai dai abin takaici shi ne, ba a aiwatar da yarjejeniyoyin yadda ya kamata ba, kuma kasashen Turai da Amurka ma sun gaza cika alkawuransu, na taimakawa kasashe masu tasowa wajen tinkarar sauyin yanayi.

Rashin hallarar shugabannin kasashen yamma a wajen taron, ya shaida yadda suke rashin girmama kasashen Afirka a kullum, baya ga kuma yadda suke gudun daukar nauyin da ke bisa wuyansu. Ba kawai sauyin yanayi na shafar makomar kasashen Afirka ba ne, har ma yana shafar makomar bai daya ta ‘yan Adam da ta duniyarmu baki daya.

Kamar dai yadda Amina Mohammed, mataimakiyar babban sakataren MDD ta bayyana a wajen taron, “da fika-fikai biyu ne tsuntsu ke iya tashi”, dole ne kasashen Yamma su gane cewa, makomar dan Adam daya ce, kuma su cika alkawuran da suka dauka, tare da daukar nauyin da ke bisa wuyansu, ta fannin daidaita matsalar sauyin yanayi.”(Mai Zane:Mustapha Bulama)

Kasashen yamma
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji
Daga Birnin Sin

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina
Daga Birnin Sin

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Next Post
Biyayya Ga Umarnin Allah Ne Kadai Zai Kawo Karshen Matsalolin Nijeriya —Sheikh Yusuf Ali

Biyayya Ga Umarnin Allah Ne Kadai Zai Kawo Karshen Matsalolin Nijeriya —Sheikh Yusuf Ali

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

June 26, 2026
Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.