• English
  • Business News
Wednesday, October 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaushe Tauraruwar Mbappe Za Ta Fara Haskawa A Madrid?

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago

Tun bayan komawar dan wasa Kylian Mbappe Real Madrid masu sharhi suka dinga hasashen irin gudunmawar da dan wasan zai iya ba wa kungiyar kasancewarsa kwararre wajen iya jefa kwallo a raga da kuma iya sarrafa kwallo.

Kawo yanzu dai sabon dan wasan da Real Madrid ta dauka a bana, Kylian Mbapppe ya buga wasanni biyu a La Liga ba tare da cin kwallo ba, matakin da wasu suke ganin kamar akwai alamun damuwa kasancewarsa sananne wajen zura kwallaye a raga a kungiyar da ya baro ta PSG.

  • Mbappe Zai Sa Riga Mai Lamba 9 A Sabuwar Kungiyarsa
  • Ko Zuwan Mbappe Zai Dusashe Tauraruwar Bellingham A Real Madrid?

Mbappe ya fara karawa a babbar gasar Sifaniya ranar Lahadi 18 ga watan Agusta a gidan Real Mallorca, inda suka tashi 1-1, sannan a ranar Lahadi 25 ga watan Agusta, Real Madrid ta fara wasan farko a bana a Santiago Bernabeu, amma na biyu a La Liga a bana kuma Real Madrid din ta doke Real Balladolid da ci 3-0, inda Federico Balberde da Brahim Diaz da kuma Endrick suka ci mata kwallayen.

Koda yake kafin fara La Liga ta 2024/25, Real Madrid ta lashe UEFA Super Cup, bayan da ta ci Atalanta 2-0 a Birnin Warsaw a Poland ranar 14 ga watan Agusta, kuma Kylian Mbappe ne ya ci wa Real kwallo ta biyu a wasan, bayan Federico Balberde da ya fara zura ta farko da ya bai wa Real Madrid damar lashe kofin farko a kakar nan.

Mbappe ya fara buga La Liga a Bernabeu a karon farkko ranar Lahadi, koda yake an sauya shi da Endrick, wanda ya ci kwallo ta uku a karawar, sannan bayan tashi daga wasan Mbappe ya ce ya ji dadin wasan ya kuma yaba ga magoya baya, yadda suke karfafaawa kungiyar gwiwa.

LABARAI MASU NASABA

Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta

Kano Pillars Ta Dakatar Da Manyan Masu Horas Da ‘Yan Wasanta Saboda Rashin Nasara

Ya kuma ce abin farin ciki sun samu maki uku a wasan, sannan za su daura dammarar lashe sauran karawar da take gabansu tare da ganin sun yi iya yin su wajen ganin sun lashe gasar Laliga da gasar cin kofin Zakarun Turai.

Mbappe ya koma Real Madrid kan fara kakar bana, bayan da yarjejeniyarsa ta kare a Paris St Germain a karshen kakar da ta wuce sai dai wasu na cewa kyaftin din tawagar Faransan mai kofin duniya ya koma Real Madrid ne, domin kwadayin lashe Champions League da kyautar Ballon d’Or.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta
Labarai

Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta

October 20, 2025
Kano Pillars Ta Dakatar Da Manyan Masu Horas Da ‘Yan Wasanta Saboda Rashin Nasara
Wasanni

Kano Pillars Ta Dakatar Da Manyan Masu Horas Da ‘Yan Wasanta Saboda Rashin Nasara

October 20, 2025
Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu
Wasanni

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Next Post
KANSIEC Ta Sauya Lokacin Zaben Kananan Hukumomin Kano Zuwa Oktoba 

KANSIEC Ta Sauya Lokacin Zaben Kananan Hukumomin Kano Zuwa Oktoba 

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

October 21, 2025
Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

October 21, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Gwamna Yusuf Ya Buƙaci Hukumar NBC Da Ta Sa Ido Kan Gidajen Rediyo Da Talabijin Na Yanar Gizo

October 21, 2025
Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

October 21, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Tabbatar Da Yusuf A Matsayin Sabon Shugaban NPC, Wasu 2 A Matsayin Kwamishinoni

October 21, 2025
Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

October 21, 2025
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Ma’aikatan Manyan Makarantu Na Kaduna Sun Dakatar Da Yajin Aiki Yayin Da Gwamna Sani Ya Amince Da Sabon Tsarin Albashi

October 21, 2025
Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

October 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.