ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaushe Tauraruwar Mbappe Za Ta Fara Haskawa A Madrid?

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago

Tun bayan komawar dan wasa Kylian Mbappe Real Madrid masu sharhi suka dinga hasashen irin gudunmawar da dan wasan zai iya ba wa kungiyar kasancewarsa kwararre wajen iya jefa kwallo a raga da kuma iya sarrafa kwallo.

Kawo yanzu dai sabon dan wasan da Real Madrid ta dauka a bana, Kylian Mbapppe ya buga wasanni biyu a La Liga ba tare da cin kwallo ba, matakin da wasu suke ganin kamar akwai alamun damuwa kasancewarsa sananne wajen zura kwallaye a raga a kungiyar da ya baro ta PSG.

  • Mbappe Zai Sa Riga Mai Lamba 9 A Sabuwar Kungiyarsa
  • Ko Zuwan Mbappe Zai Dusashe Tauraruwar Bellingham A Real Madrid?

Mbappe ya fara karawa a babbar gasar Sifaniya ranar Lahadi 18 ga watan Agusta a gidan Real Mallorca, inda suka tashi 1-1, sannan a ranar Lahadi 25 ga watan Agusta, Real Madrid ta fara wasan farko a bana a Santiago Bernabeu, amma na biyu a La Liga a bana kuma Real Madrid din ta doke Real Balladolid da ci 3-0, inda Federico Balberde da Brahim Diaz da kuma Endrick suka ci mata kwallayen.

ADVERTISEMENT

Koda yake kafin fara La Liga ta 2024/25, Real Madrid ta lashe UEFA Super Cup, bayan da ta ci Atalanta 2-0 a Birnin Warsaw a Poland ranar 14 ga watan Agusta, kuma Kylian Mbappe ne ya ci wa Real kwallo ta biyu a wasan, bayan Federico Balberde da ya fara zura ta farko da ya bai wa Real Madrid damar lashe kofin farko a kakar nan.

Mbappe ya fara buga La Liga a Bernabeu a karon farkko ranar Lahadi, koda yake an sauya shi da Endrick, wanda ya ci kwallo ta uku a karawar, sannan bayan tashi daga wasan Mbappe ya ce ya ji dadin wasan ya kuma yaba ga magoya baya, yadda suke karfafaawa kungiyar gwiwa.

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe

Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati

Ya kuma ce abin farin ciki sun samu maki uku a wasan, sannan za su daura dammarar lashe sauran karawar da take gabansu tare da ganin sun yi iya yin su wajen ganin sun lashe gasar Laliga da gasar cin kofin Zakarun Turai.

Mbappe ya koma Real Madrid kan fara kakar bana, bayan da yarjejeniyarsa ta kare a Paris St Germain a karshen kakar da ta wuce sai dai wasu na cewa kyaftin din tawagar Faransan mai kofin duniya ya koma Real Madrid ne, domin kwadayin lashe Champions League da kyautar Ballon d’Or.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe
Wasanni

Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe

November 14, 2025
Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati
Wasanni

Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati

November 14, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4
Manyan Labarai

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
Next Post
KANSIEC Ta Sauya Lokacin Zaben Kananan Hukumomin Kano Zuwa Oktoba 

KANSIEC Ta Sauya Lokacin Zaben Kananan Hukumomin Kano Zuwa Oktoba 

LABARAI MASU NASABA

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025
BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.