• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaushe Tauraruwar Mbappe Za Ta Fara Haskawa A Madrid?

by Abba Ibrahim Wada
10 months ago
in Wasanni
0
Yaushe Tauraruwar Mbappe Za Ta Fara Haskawa A Madrid?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun bayan komawar dan wasa Kylian Mbappe Real Madrid masu sharhi suka dinga hasashen irin gudunmawar da dan wasan zai iya ba wa kungiyar kasancewarsa kwararre wajen iya jefa kwallo a raga da kuma iya sarrafa kwallo.

Kawo yanzu dai sabon dan wasan da Real Madrid ta dauka a bana, Kylian Mbapppe ya buga wasanni biyu a La Liga ba tare da cin kwallo ba, matakin da wasu suke ganin kamar akwai alamun damuwa kasancewarsa sananne wajen zura kwallaye a raga a kungiyar da ya baro ta PSG.

  • Mbappe Zai Sa Riga Mai Lamba 9 A Sabuwar Kungiyarsa
  • Ko Zuwan Mbappe Zai Dusashe Tauraruwar Bellingham A Real Madrid?

Mbappe ya fara karawa a babbar gasar Sifaniya ranar Lahadi 18 ga watan Agusta a gidan Real Mallorca, inda suka tashi 1-1, sannan a ranar Lahadi 25 ga watan Agusta, Real Madrid ta fara wasan farko a bana a Santiago Bernabeu, amma na biyu a La Liga a bana kuma Real Madrid din ta doke Real Balladolid da ci 3-0, inda Federico Balberde da Brahim Diaz da kuma Endrick suka ci mata kwallayen.

Koda yake kafin fara La Liga ta 2024/25, Real Madrid ta lashe UEFA Super Cup, bayan da ta ci Atalanta 2-0 a Birnin Warsaw a Poland ranar 14 ga watan Agusta, kuma Kylian Mbappe ne ya ci wa Real kwallo ta biyu a wasan, bayan Federico Balberde da ya fara zura ta farko da ya bai wa Real Madrid damar lashe kofin farko a kakar nan.

Mbappe ya fara buga La Liga a Bernabeu a karon farkko ranar Lahadi, koda yake an sauya shi da Endrick, wanda ya ci kwallo ta uku a karawar, sannan bayan tashi daga wasan Mbappe ya ce ya ji dadin wasan ya kuma yaba ga magoya baya, yadda suke karfafaawa kungiyar gwiwa.

Labarai Masu Nasaba

Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

ÆŠan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota

Ya kuma ce abin farin ciki sun samu maki uku a wasan, sannan za su daura dammarar lashe sauran karawar da take gabansu tare da ganin sun yi iya yin su wajen ganin sun lashe gasar Laliga da gasar cin kofin Zakarun Turai.

Mbappe ya koma Real Madrid kan fara kakar bana, bayan da yarjejeniyarsa ta kare a Paris St Germain a karshen kakar da ta wuce sai dai wasu na cewa kyaftin din tawagar Faransan mai kofin duniya ya koma Real Madrid ne, domin kwadayin lashe Champions League da kyautar Ballon d’Or.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FIFAFOOTBALLMbappeReal Madrid
ShareTweetSendShare
Previous Post

BUA Ya Soki Manyan Diloli Kan Dakile Shirin Sayar Da Siminti A Kan Farashi Mai Sauki

Next Post

KANSIEC Ta Sauya Lokacin Zaben Kananan Hukumomin Kano Zuwa Oktoba 

Related

Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu
Wasanni

Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

6 hours ago
ÆŠan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota
Manyan Labarai

ÆŠan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota

15 hours ago
Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea
Wasanni

Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea

2 days ago
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata
Wasanni

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

3 days ago
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari
Wasanni

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

4 days ago
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa
Wasanni

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

4 days ago
Next Post
KANSIEC Ta Sauya Lokacin Zaben Kananan Hukumomin Kano Zuwa Oktoba 

KANSIEC Ta Sauya Lokacin Zaben Kananan Hukumomin Kano Zuwa Oktoba 

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

July 3, 2025
Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

July 3, 2025
Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

July 3, 2025
Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

July 3, 2025
Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

July 3, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

July 3, 2025
Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

July 3, 2025
Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

July 3, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

July 3, 2025
Kotu Ta Yanke Wa ÆŠan TikTok Tsulange Hukuncin ÆŠauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

Kotu Ta Yanke Wa ÆŠan TikTok Tsulange Hukuncin ÆŠauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

July 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.