• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yawaitar Hadurran Mota A Hanyoyin Kasar Nan

by Sadiq
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Yawaitar Hadurran Mota A Hanyoyin Kasar Nan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Munanan hadurran mota da suka auku a lokacin bukukuwan da suka gabata wani abu ne mai tayar da hankala da ya kamata hukumomin da da lamuran suka shafa su gaggauta daukar matakin kawo karshen sake aukuwar su.

Ko a makon jiya ‘yansanda a Jiha Imo sun sanar da mutuwar wasu iyalai mutum 8 da hadarin mota ya rutsa da su a shataletalen Amanwozuzu da ke karamar hukumar Ikeduru ta Jihar Imo.

  • NIS Shiyyar Arewa Maso Gabas Ta Kaddamar Da “Operation Tsaron Iyaka”
  • Ba Wanda Zai Iya Kawo Tsaiko Ga Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

A kwanaki ma, matafiya 9 sun mutu a Jihar Osun a yayin da wata babbar mota ta saki hanya ta afka wa mutane, hakanan kuma a Jihar Kaduna wasu mutane 4 sun mutu yayin da mutum 56 suka jikkata a wani mummunan hadarin.

Wadannan na daga cikin hadurra kalilan da suka faru na lokacin bukukuwan da suka gabata a watan Disamba, 2023.

A rahoto na baya-bayan nan da Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta bayar ya nuna, ‘yan Nijeriya 24 ke mu-tuwa a kullum sakamakon hatsarin mota.

Labarai Masu Nasaba

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

Tinubu Ya Nada Ɗan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

Lamarin kuma yana kara munana ne a lokutan bukukuwa kamar kirismeti da bikin murnar sabuwar she-kara a yayin da mutane da dama suke tafiye-tafiye.

A wani rahoton kuma da Hukumar Kiyaye Hadurran Kan Titi (FRSC) ta fitar a watan Agusta na shekarar 2023, ta bayyana cewa a tsakanin watan da aka bayar da rahoton, ‘yan Nijeriya 24 su ke rika mutuwa a kullum a tsakanin watan Janairu zuwa watan Yuni na shekarar 2023.

Jimillar mutanen da suka rasa rayukansu a cikin wata 6 na shekarar 2023, kamar yadda FRSC ta ruwaito sun kai mutum 4,387, wanda hakan ke nuna da cewa, mutum ne 731 suka mutu, mutum 24 kenan a kullum.

Kafin wannan rahoto na watan Agusta, Hukumar FRSC ta bayyana cewa a watan Afrilu mutum 1,349 suka mutu sakamakon hadarin mota a tsakanin 1 ga watan Janairu, 2023 zuwa ranar 12 ga watan Afrilu na 2023.

Rahoton na watan Afrilu ya kuma bayyana cewa, a tsakanin lokacin da ake magana an yi hadari 2,463, ta kuma kara bayyana cewa, motoci 3,965 masu dauke da mutum 16,102 suka yi hadarin a lokuta daban-daban inda a cikinsu mutum 1,349 suka rasa rayukansu yayin da mutum 7,744 suka ji raunuka daban-daban.

Jami’in wayar da kan al’umma na hukumar FRSC, Bisi Kazeem, ya lura da cewa, hadurran sun auku ne a jihohi 36 na tarayyar Nijeriya da kuma yankin babban birnin tarayyar Abuja, ya kuma ce, “Daga Janairu zuwa Yuni, mutum 4,387 sauka mutu sakamakon hadurran mota yayin da kuma mutum 14,108 suka ji raunuka daban-daban.”

Abin takaici shi ne yadda ake asarar rayukan al’umma a kullum, ba a dauki rayuwa da muhimmanci ba a Nijeriya, ana kashe mutane ta hanyar gangaci amma babu wanda ake kamawa da laifin wannan ta’asar.

Amma kuma hadurran motoci sun fi yawaita a lokutan bukukuwa saboda yadda mutane ke tururuwan ganin sun koma garuruwansu na asali don gudanar da bukukuwan, abin har ya zama jiki.

Duk da mastalar tsaro da ake fuskanta a sassan Nijeriya, al’umma sun gwammace su yi tafiya ta hanyoyionmu musamman ganin yadda kudaden sufurin jirgin sama ya yi tashin gwauron zabo, ta yadda ya fi karfin talakan Nijeriya.

Amma kuma wasu da dama na tsoron tafiya ta hanyoyinmu saboda yawaitar hatsurran da ake samu wanda kuma yakan ya fi tsanani a lokutan bukukuwa.

A matsayinmu na gidan jarida muna sane da dalilan da ke kara yawaitar hadurran a manyan hanyoyin kasar nan, wadanda suka hada da ko dai halin da hanyoyin ke ciki da kuma halin da motocin ke ciki ko kuma gangaci daga masu tukin.

Duk da cewa, wasu dalilan na taimakawa wajen afkuwar hadurra a hanyoyinmu amma matsalar rashin kyawun hanyoyinmu ne a kan gaba wajen haifar da hatsurra a kasar nan.

In ka duba Gabas, Arewa, kudu da yammancin kasar duk lamarin daya ne, hanyoyin sun lalace. Hanyoyin Nijeriya sun yi lalacewar da a wasu wuraren manyan ramuka masu zurfi ne suka mamaye su gaba daya.

Rashin ingancin motocin da ake amfani da su shi ma babbar matsala ne da ya kamata a kawo wa dauki. In an sa ido yadda ya kamata za a iya rage motocin da ba su da lafiyar da ta kamata a hau hanya don yin tafiye-tafiye da su.

Sa ido don gano motocin da suke da matsala da kuma tsaurara hanyoyin karbar lasisi na da muhim-manci. Haka kuma ya kamata a kara horas da jami’an kula da motoci tare da ba su karfin kawar da mo-tocin da suka karya doka daga hanyoyinmu.

Haka kuma dole direbobi su kula yayin da suke a kan hanya don kauce wa aukuwar hadari, su bi duk-kan dokokin hanya tare da mutunta sauran masu amfani da hanyar.

Akwai bukatar jami’an FRSC da jami’an ‘yansanda su tabbatar da hukunta masu karya dokokin hanya, kamar masu gudun wuce kima da wuce moto ba bi sa ka’ida ba.

A kan haka, wannan jaridar ke kira ga dukkan masu ruwa da tsaki da su dauki matakan kariya daga af-kuwar hadari a kan hanyoyinmu da matukar muhimmanci.

Ya kamata gwamnati ta jagoranci kawo karshen mace-mace da raunukan da ake ji a hanyoyinmu, lokaci ya yi da za a dauki kwakkwaran mataki, ‘yan Nijeriya sun cancanci samun hanyoyi ba tare da fargabar hadari ba a lokutan bukukuwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Abdilahi Ismail Abdilahi: Furucin Xi Jinping Ya Burge Ni Matuka

Next Post

Garkuwa Da Mutane Na Kara Ta’azzara A Nijeriya

Related

APC
Manyan Labarai

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

9 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nada Ɗan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

23 hours ago
Sojoji Sun Daƙile Wani Harin Ta’addanci Tare Da Cafke Wasu Mutum Biyu A Taraba
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Wani Harin Ta’addanci Tare Da Cafke Wasu Mutum Biyu A Taraba

1 day ago
Buhari 1942 – 2025: Rayuwarsa, Rasuwarsa, Jana’izarsa, Da Ci gaba Da Ta’aziyya
Manyan Labarai

Buhari 1942 – 2025: Rayuwarsa, Rasuwarsa, Jana’izarsa, Da Ci gaba Da Ta’aziyya

1 day ago
Natasha Ta Rubuta Wa Majalisa, Tana Neman A Yi Biyayya Ga Umarnin Kotu
Manyan Labarai

Natasha Ta Rubuta Wa Majalisa, Tana Neman A Yi Biyayya Ga Umarnin Kotu

2 days ago
Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ
Tsaro

Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ

2 days ago
Next Post
Garkuwa Da Mutane Na Kara Ta’azzara A Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Kara Ta'azzara A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Ciwon Baya Yayin Goyon Ciki Da Hanyar Magance Shi

Dalilin Ciwon Baya Yayin Goyon Ciki Da Hanyar Magance Shi

July 19, 2025
UTME

An Samu Rarrabuwar Kai Kan Makin Shiga Manyan Makarantu

July 19, 2025
Jami’ar Ilorin Ta Karrama Shugabannin JAMB, THISDAY Da Wasu 63 A Bikin Shekara 50

Jami’ar Ilorin Ta Karrama Shugabannin JAMB, THISDAY Da Wasu 63 A Bikin Shekara 50

July 19, 2025
‘Yansanda Sun Hana Gudanar Da Taron Tunawa Da Ranar Haihuwar Obi A Kaduna

‘Yansanda Sun Hana Gudanar Da Taron Tunawa Da Ranar Haihuwar Obi A Kaduna

July 19, 2025
Abinci

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

July 19, 2025
sallah

Yadda Hauhawar Farashin Kayan Abinci Ya Ragu A Nijeriya

July 19, 2025
Shettima

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

July 19, 2025
Fyade

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

July 19, 2025
APC

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

July 19, 2025
Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.