• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaya Kuri’un Yankin Arewa Maso Yamma Za Su Kasance A 2023?

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
A woman votes at a polling station in Kano, Nigeria, March 28, 2015. Many Nigerians fear a clash along religious, ethnic, and sectional lines regardless of the result of the presidential race between incumbent Goodluck Jonathan, a Christian from the south, and Muhammadu Buhari, a former military ruler and Muslim northerner. (Samuel Aranda/The New York Times)

A woman votes at a polling station in Kano, Nigeria, March 28, 2015. Many Nigerians fear a clash along religious, ethnic, and sectional lines regardless of the result of the presidential race between incumbent Goodluck Jonathan, a Christian from the south, and Muhammadu Buhari, a former military ruler and Muslim northerner. (Samuel Aranda/The New York Times)

A ko da yaushe zabe a Nijeriya ya kan kasance ne bisa la’akari da kuri’un da ake jefawa a yankuna.

Wannan lamari ne da ke turnike zaben kasar nan tun a shekarar 1959 lokacin da yankin arewa ya fi samun kujeru masu yawa da aka amince na yin sulhu wajen hawa karagar mulki.

  • Kashi 31 Na ‘Yan Nijeriya Ba Su Iya Karatu Da Rubutu Ba ― Gwamnatin Tarayya
  • Kwastam Ta Damke Mazakutar Jaki 7000 Da Miyagun Kwayoyi A Legas

Tun bayan da kawo mulkin dimokuradiyya, yankin arewa yana taka muhimmin rawa a cikin harkokin dimokuradiyyar kasar nan.

Mafi yawancin shugabannin da suka lashe zabe dole ne sai sun samu nasara a yankin arewa maso yammacin Nijeriya, duk da ba shi ne samun nasara na karshe a zabe ba.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya dade yana samun nasara a yankin arewa maso yamma, tun a shekarar 2003 mafi yawancin abokan karawarsa suna faduwa zabe a wannan yankin.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

Yankin arewa maso yamma ta hada wasu jihohin da suke da harafin K har guda hudu, Kano, Kaduna, Katsina da Kebbi, wanda suke iya samar wa dan takara sama da kuri’u miliyan uku, wannan ya danganta ne da yanayin dan takarar.

Mafi yawancin ‘yan takara suna lashe zabe ne a tsakanin kuri’u miliyan 15 zuwa 17, sai dai Jonathan da ya samu kuri’u miliyan 20, wanda ba a taba samu ba tun bayan shekaru 10 da suka gabata.

Yankin arewa maso yamma ya kasance yankin da ake bai wa ‘yan takara dauki, sai dai kabalanci da addini suna taka muhimmiyar rawa a yankin.

Ba za a taba musanta cewa ‘yan Nijeriya suna amfani da kabila da addini wajen zaben dan takara ba.

Sai dai abin da yafi dacewa shi ne, samun kasa daya ba tare da la’akari da yanki ko addini ba.

Abun tambaya a nan shi ne, ina kuri’an yankin arewa maso yamma za su kasance? Wasu na ganin cewa Tinunbu yana da tabbacin lashe wannan yankin, amma tambayan ita ce, ta ina zai iya samun nasarar? Wannan lokaci ne kadai zai iya tabbatar da haka.

Wasu na ganin cewa an samu sauyin jefa kuri’a a yankin arewa maso yamma sakamakon irin kiraye-kirayen da malaman addini ke yi.

Haka kuma wasu ‘yan siyasa a yankin arewa sun dage a kan sai mulki ya dawo arewa ta hannun Atiku, inda suka tabbatar da cewa kuri’un yankin arewa maso yamma za su kasance na Atiku ne.

Wasu kuma na ganin Peter Obi da Kwankwaso na iya taka rawa a wannan yankin. Bayan addni da kala da suke da tasiri a yankin arewa maso yamma, kudade ma za su taka muhimmiyar rawa a yankin.

Wasu na ganin cewa wannan ita ce siyasa mafi tsada da za a gudanar a kasar nan.

A yanzu da ya rage saura kasa da kwani 170 a gudanar da zabe, abu guda daya shi ne, duk wanda ya lashe yankin arewa maso yamma shi zai ci nasara a zabe? Lokaci ne kadai zai iya tabbatar da haka.

A yawan masu rajista da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta fitar, yankin arewa maso yamma shi ke kan gaba, inda yake da yawan masu jefa kuri’a guda 22,672,373.

Wannan bayani yana cikin shafin hukumar INEC, inda ta nuna cewa ta samu karin masu rajistar zabe guda 12,298,932 a zaben 2023.

Gaba daya jimillar jihohin arewa masu yamma sun hada da Jigawa, Kaduna, Katsina, Kano, Kebbi, Sakkwato da kuma Zamfara, da suke da yawan masu jefa kuri’a guda 22,672,373 a zaben 2023.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Next Post
Shugaba Xi Ya Taya João Lourenço Murnar Lashe Zaben Shugaban Angola

Shugaba Xi Ya Taya João Lourenço Murnar Lashe Zaben Shugaban Angola

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.