ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaya Kuri’un Yankin Arewa Maso Yamma Za Su Kasance A 2023?

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
A woman votes at a polling station in Kano, Nigeria, March 28, 2015. Many Nigerians fear a clash along religious, ethnic, and sectional lines regardless of the result of the presidential race between incumbent Goodluck Jonathan, a Christian from the south, and Muhammadu Buhari, a former military ruler and Muslim northerner. (Samuel Aranda/The New York Times)

A woman votes at a polling station in Kano, Nigeria, March 28, 2015. Many Nigerians fear a clash along religious, ethnic, and sectional lines regardless of the result of the presidential race between incumbent Goodluck Jonathan, a Christian from the south, and Muhammadu Buhari, a former military ruler and Muslim northerner. (Samuel Aranda/The New York Times)

A ko da yaushe zabe a Nijeriya ya kan kasance ne bisa la’akari da kuri’un da ake jefawa a yankuna.

Wannan lamari ne da ke turnike zaben kasar nan tun a shekarar 1959 lokacin da yankin arewa ya fi samun kujeru masu yawa da aka amince na yin sulhu wajen hawa karagar mulki.

  • Kashi 31 Na ‘Yan Nijeriya Ba Su Iya Karatu Da Rubutu Ba ― Gwamnatin Tarayya
  • Kwastam Ta Damke Mazakutar Jaki 7000 Da Miyagun Kwayoyi A Legas

Tun bayan da kawo mulkin dimokuradiyya, yankin arewa yana taka muhimmin rawa a cikin harkokin dimokuradiyyar kasar nan.

ADVERTISEMENT

Mafi yawancin shugabannin da suka lashe zabe dole ne sai sun samu nasara a yankin arewa maso yammacin Nijeriya, duk da ba shi ne samun nasara na karshe a zabe ba.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya dade yana samun nasara a yankin arewa maso yamma, tun a shekarar 2003 mafi yawancin abokan karawarsa suna faduwa zabe a wannan yankin.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

Yankin arewa maso yamma ta hada wasu jihohin da suke da harafin K har guda hudu, Kano, Kaduna, Katsina da Kebbi, wanda suke iya samar wa dan takara sama da kuri’u miliyan uku, wannan ya danganta ne da yanayin dan takarar.

Mafi yawancin ‘yan takara suna lashe zabe ne a tsakanin kuri’u miliyan 15 zuwa 17, sai dai Jonathan da ya samu kuri’u miliyan 20, wanda ba a taba samu ba tun bayan shekaru 10 da suka gabata.

Yankin arewa maso yamma ya kasance yankin da ake bai wa ‘yan takara dauki, sai dai kabalanci da addini suna taka muhimmiyar rawa a yankin.

Ba za a taba musanta cewa ‘yan Nijeriya suna amfani da kabila da addini wajen zaben dan takara ba.

Sai dai abin da yafi dacewa shi ne, samun kasa daya ba tare da la’akari da yanki ko addini ba.

Abun tambaya a nan shi ne, ina kuri’an yankin arewa maso yamma za su kasance? Wasu na ganin cewa Tinunbu yana da tabbacin lashe wannan yankin, amma tambayan ita ce, ta ina zai iya samun nasarar? Wannan lokaci ne kadai zai iya tabbatar da haka.

Wasu na ganin cewa an samu sauyin jefa kuri’a a yankin arewa maso yamma sakamakon irin kiraye-kirayen da malaman addini ke yi.

Haka kuma wasu ‘yan siyasa a yankin arewa sun dage a kan sai mulki ya dawo arewa ta hannun Atiku, inda suka tabbatar da cewa kuri’un yankin arewa maso yamma za su kasance na Atiku ne.

Wasu kuma na ganin Peter Obi da Kwankwaso na iya taka rawa a wannan yankin. Bayan addni da kala da suke da tasiri a yankin arewa maso yamma, kudade ma za su taka muhimmiyar rawa a yankin.

Wasu na ganin cewa wannan ita ce siyasa mafi tsada da za a gudanar a kasar nan.

A yanzu da ya rage saura kasa da kwani 170 a gudanar da zabe, abu guda daya shi ne, duk wanda ya lashe yankin arewa maso yamma shi zai ci nasara a zabe? Lokaci ne kadai zai iya tabbatar da haka.

A yawan masu rajista da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta fitar, yankin arewa maso yamma shi ke kan gaba, inda yake da yawan masu jefa kuri’a guda 22,672,373.

Wannan bayani yana cikin shafin hukumar INEC, inda ta nuna cewa ta samu karin masu rajistar zabe guda 12,298,932 a zaben 2023.

Gaba daya jimillar jihohin arewa masu yamma sun hada da Jigawa, Kaduna, Katsina, Kano, Kebbi, Sakkwato da kuma Zamfara, da suke da yawan masu jefa kuri’a guda 22,672,373 a zaben 2023.

Arewa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
Shugaba Xi Ya Taya João Lourenço Murnar Lashe Zaben Shugaban Angola

Shugaba Xi Ya Taya João Lourenço Murnar Lashe Zaben Shugaban Angola

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.