• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yuan (RENMINBI) Na Ci Gaba Da Samun Farin Jini A Kasashen Afirka 

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Yuan (RENMINBI) Na Ci Gaba Da Samun Farin Jini A Kasashen Afirka 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasashe da dama na nahiyar Afirka sun jima da kulla dangantakar cinikayya da China, ta yadda zai kasance abu mawuyaci a samu gidan da ba a amfani da kayan da aka kera a kasar Sin. To sai dai sakamakon kakagidan da dalar Amerika ta yi a harkokin cinikayya na kasa da kasa ya sanya ake samun tarnaki a harkokin kasuwanci tsakanin wannan kasa da waccan kasa.

Tun fil azal, akwai dadaddiyar alakar cinikayya tsakanin China da Nijeriya, hasali ma dai China ita ce babbar kasa da ta fi kowace kasa huldar kasuwanci da Nijeria. Hada-hadar kasuwanci tsakanin China da Nijeriya ta kasance mai armashi, kuma mai amfanar dukkan bangarorin biyu. Bisa ga wannan dalili ne China da Nijeriya suka ga akwai bukatar rage dogaro da dalar Amerika wajen gudanar da cinikayya tsakaninsu.

  • Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida
  • Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

Don haka kasashen biyu suka kirkiro da wani tsari kan yarjejeniyar musayar kudadensu, abin da zai baiwa Nijeriya damar yin amfani da Yuan, wato Renminbi kai tsaye wajen sayen kayayyaki daga China ba tare da yin amfani da dalar Amerika ba. An ko kirkiro da wannan tsari ne tun watan Afrilun shekarar 2018, wanda aka sabunta a watan Afrilun shekarar 2021, sannan kuma aka sake sabunta shi a karshen watan Disamban shekarar 2024.

Kudin Sin Yuan ya kasance daya daga cikin kudaden da hukumar bayar da lamuni ta kasa da kasa IMF ta amince da su. Wannan karbuwa da Yuan ta samu ya kara daga darajarta tare da samun karbuwa tsakanin kasashen duniya.

Aiwatar da wannan tsari yadda ya kamata, zai bunkasa cinikayya tsakanin Nijeriya da kasar Sin, tattalin arzikin Nijeriya zai samu tagomashi tare da samun karuwar aikin yi ga miliyoyin ’yan Nijeriya. Kana zai habaka zuba jari a fannoni daban daban tsakanin kasashen biyu, tare da rage dogaro da dalar Amerika. Wannan zai baiwa China da Nijeriya damar yaukaka dangantaka ta fannin kudade ta yadda hada hadar cinikayya za ta kasance babu tarnaki. ( Lawal Mamuda)

Labarai Masu Nasaba

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

A Daina Gaggawar Murnar Samun Nasara Kan Ta’addanci A Nijeriya


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta

Next Post

Nazarin CGTN: Neman Kashe Kaso 5 Na GDP Kan Tsaro Ya Nuna Rashin Dabara Na NATO

Related

Fyade
Ra'ayinmu

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

2 weeks ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Ra'ayinmu

A Daina Gaggawar Murnar Samun Nasara Kan Ta’addanci A Nijeriya

3 weeks ago
Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu
Ra'ayi Riga

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

3 weeks ago
Kura Za Ta Ce Da Kare Maye
Ra'ayi Riga

Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

4 weeks ago
Ra'ayinmu

Bukatar Hukunta Masu Jagorantar Kashe-kashe A Nijeriya

2 months ago
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)
Ra'ayinmu

Akwai Bukatar Daina Cin Zarafin Malaman Makaranta

2 months ago
Next Post
Nazarin CGTN: Neman Kashe Kaso 5 Na GDP Kan Tsaro Ya Nuna Rashin Dabara Na NATO

Nazarin CGTN: Neman Kashe Kaso 5 Na GDP Kan Tsaro Ya Nuna Rashin Dabara Na NATO

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.