• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yunkurin Magance Dalar Shara A Kano

by Muhammad Awwal Umar
2 years ago
in Rahotonni
0
Yunkurin Magance Dalar Shara A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsawon lokaci a jihar Kano, duk inda ka duba sako da lungu musamman cikin birni, ban da tsibiri tsibiri na taragon shara, ba ka yin tozali da komai. An ta gabatar da tarin dalilai mabanbanta da ake tsammanin sune suka jaza wanzuwar wannan annakiya ta shara cikin birnin na Kano, duk da hadarin da take da shi ga fannin lafiyar jama’ar jihar. Ko babu komai, cutar maleriya ta sauro da kuma yiwuwa 6arkewar cutar kwalara, duka suna da alaka ta kusa da barin shara barkatai a muhallan jama’a ba tare da kawar da ita ba.

Illar barin shara barkatai a tsakanin al’uma, sha’anin ya kere batun 6arkewar cutuka ne kawai, lamarin kan yi sanadiyyar kawo ambaliyar ruwa, yayinda magudanan ruwan suka cushe, ba tare da an kawar da sharar da ta shake su ba. Duba da irin wadannan dalilai, duk wani shugaba, zai kwana ne da sanin wajibcin kawar da duk wata sharar da barin ta zai iya cutar da jama’ar da ke karkashinsa ta fuskoki da dama. Saboda barazanar da cakudin shara ke wa jama’ar ta Kano, shi ne babban dalilin da ya fizge mu zuwa ga jin ta-bakin babban daraktan hukumar kula da debe shara ta Kano a yau, wato Ambassador Alhaji Ahmadu Haruna Zago, wanda a fagen siyasar Kano aka fi saninsa da Danzago.

  • Malamai Sun Gargadi Tinubu Kan Daukar Matakin Soji A Kan Nijar
  • Mai Magana Da Yawun Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Yi Karin Haske Kan Bayanan Kafofin Watsa Labarai Game Da Sanarwar Italiya Na Kin Tsawaita Yarjejeniyar Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

Ambassador Danzago, ya yi wata shimfida ne yayin tattaunawar tamu, inda ya faro tun daga Shekarar 1999, lokacin da Engr Rabi’u Musa Kwankwaso ne gwamnan Kano. Har Kwankwason ya bar kujerar mulkin ta Kano, wannan ma’aikata ta shara na amsa sunan REMASAB (Kano State Refuse Management & Sanitation Board) ne. Haka, shi ma Malam Shekarau, tun da yake bisa kujerar gwamnan Kano, daga Shekarar 2003 zuwa 2011, bai canja sunan hukumar ba. Bugu da kari, da Kwankwaso da Shekarau, duka sun yi kokarin samar da kayan aiki ga wannan hukuma ta shara. Sannan, sa’adda maigirma Engr. Dr Rabi’u Musa Kwankwaso ya dawo zangon mulkinsa na biyu a Shekarar 2015,  ya sake gwangwaje wannan hukuma ta Remasab da kayan aiki, irin wadanda ake matukar kishirwarsu a lokacin. Sabbin mabanbantan motoci kar na aikin shara kimanin guda arba’in da biyar (45) ne ya danka su ga hukumar ta Remasab. Sannan, har ya sauka, hukumar na karkashin kulawar gwamnati ne, damfare da sunanta da ta yi shuhura da shi, wato Remasab.

Ambassador Danzago ya kara da cewa,  tsohon gwamna Ganduje kuwa, wanda ya dare bisa kujerar gwamnan Kano a Shekarar 2019 zuwa 2023, ya sami hukumar ta Remasab karkashin kulawar gwamnatin Kano ne, amma gabanin saukarsa, sai ya gabatar da wata yarjejeniya tsakanin gwamnati da wani kamfani, ta yadda hukumar za ta tashi karkashin kulawar gwamnati zuwa ga wasu tsirarin mutane. Sai dai, tun kafin a je da nisa, sai wannan yarjejeniya ta ruguje, ko dai saboda wata kuskunda da aka samu ne daga wancan kamfani, ko kuma, watakil gwamnati ba ta tsaya tsai ta nazarci lamarin ba irin yadda ya kamata.

Ko da maigirma gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya sami damar zama za6a66en gwamnan wannan jiha tamu ta Kano, sai ya nuna fa da gaske yake wajen yin duk mai yiwuwa wajen kawar da kazantar sharar da ta yi wa jihar Kano katutu ba tare da yin wata kasa a gwiwa ba, in ji Danzago. Sannan, tsohon sunan da aka san ma’aikatar da shi tun azal, wato Remasab, nan take sabon gwamna ya lashi takobin dawo mata da shi, tare da yin iya iyawarsa wajen dawo da wannan ma’aikata cikin haiyacinta.

Labarai Masu Nasaba

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

A kan hanyar cika kudirin gwamna na farfado da ran wannan ma’aikata in ji Danzago, shi ma shugaban hukumar sauraren korafe korafen jama’a ta Kano, Muhuyi Magaji R/Gado, ya shiga ya fita, har sai da ya dawowa da wannan hukuma wasu manyan motoci nata guda bakwai (7) da ma wasu, wadanda a baya aka sai da su ba bisa ka’ida ba. Yanzu haka, mun sa motocin na gudanar da aiyukansu a hukumar. Da yawan kayan wannan hukuma da aka sayar, Muhuyin, ya yi azamar dawo mana da su alhamdulillaHi.

Idan ba a manta ba, cikin wata jarida ta yanar gizo da ake kiranta da Dailynigerian.com, an jiyo mai magana da yawun gwamnan Kano, Sanusi Bature D/Tofa na gabatar da wani zargi da ake yi wa tsohuwar gwamnatin Ganduje, na sayar da akasarin manyan kadarorin wannan hukuma ta Remasab,  cikin fakewa da kulla ciniki na hadin gwiwa tsakanin gwamnati da wani kamfani, an sayar da su ne ga iyalai da kuma abokai, inda maigirma gwamnan Kano Abba Kabir ke fassara lamarin da wani abin kaico!.

Haka zalika, za mu yi duk mai yiwuwa, wajen ganin cewa iya wuraren da hukuma ta sahale ne kawai za a zuba shara a wurin. Ko alama, ba za mu lamunci jirkitar da shara barkatai a ko’ina cikin birni da kewaye ba, in ji Danzago.

Danzagon ya ci gaba da cewa,  mu na aiki ne yanzu haka dare da rana ba tare da kakkautawa ba. Dole ne shugaba ya fita, ba ya makale cikin ofis ba, ba tare da sanin abinda ke faruwa a waje ba. Shi shugaba, shi ne mai yi wa mutane hidima a ko da yaushe. Shi yasa lokacin da muka shiga aiki can “Yan dabino Yakasai lokacin da ake lafta mamakon ruwa, sai jama’ar unguwar suka rika mamakinmu. Ba wannan ma’aikata tawa ta Remasab ba kawai, kusan kowace ma’aikata na bisa sirdin aiwatar da aiyuka ne, duba da kalaman gwamna cewa, zuwa Watanni shida, duk wani da aka nada bisa wata kujera sai bai yi abin kirki ba, a fili ne yake cewa wannan mutumi ya sallami kansa da kansa.

Ambassador Danzago ya kara da cewa, yanzu haka suna nan suna tantance hakikanin ma’aikatansu a takarda, kuma za su bi su har wuraren da suke aiki don tabbatarwa. Bugu da kari, duk wani ma’aikacinmu da ke da wani hakki na gaskiya, a shirye muke da mu ba shi hakkin nasa.

Babu shakka, muddin kowace ma’aikata za ta tashi haikan wajen sauke nauyin da maigirma gwamna Abba Kabir Yusuf ya aza mata, la-budda za a haife da-mai-ido a Kano.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kallon-kallon: Kungiyar ‘Yan Kwadago Da ‘Yan Nijeriya

Next Post

Manchester United Za Ta Bayyana Matsayarta A Kan Greenwood

Related

jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

3 weeks ago
Kano
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

3 weeks ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

4 weeks ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

1 month ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

1 month ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

1 month ago
Next Post
Manchester United Za Ta Bayyana Matsayarta A Kan Greenwood

Manchester United Za Ta Bayyana Matsayarta A Kan Greenwood

LABARAI MASU NASABA

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

July 1, 2025
Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

July 1, 2025
Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

July 1, 2025
Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

July 1, 2025
Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.