ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yunkurin Magance Dalar Shara A Kano

by Muhammad Awwal Umar
3 years ago
Kano

Tsawon lokaci a jihar Kano, duk inda ka duba sako da lungu musamman cikin birni, ban da tsibiri tsibiri na taragon shara, ba ka yin tozali da komai. An ta gabatar da tarin dalilai mabanbanta da ake tsammanin sune suka jaza wanzuwar wannan annakiya ta shara cikin birnin na Kano, duk da hadarin da take da shi ga fannin lafiyar jama’ar jihar. Ko babu komai, cutar maleriya ta sauro da kuma yiwuwa 6arkewar cutar kwalara, duka suna da alaka ta kusa da barin shara barkatai a muhallan jama’a ba tare da kawar da ita ba.

Illar barin shara barkatai a tsakanin al’uma, sha’anin ya kere batun 6arkewar cutuka ne kawai, lamarin kan yi sanadiyyar kawo ambaliyar ruwa, yayinda magudanan ruwan suka cushe, ba tare da an kawar da sharar da ta shake su ba. Duba da irin wadannan dalilai, duk wani shugaba, zai kwana ne da sanin wajibcin kawar da duk wata sharar da barin ta zai iya cutar da jama’ar da ke karkashinsa ta fuskoki da dama. Saboda barazanar da cakudin shara ke wa jama’ar ta Kano, shi ne babban dalilin da ya fizge mu zuwa ga jin ta-bakin babban daraktan hukumar kula da debe shara ta Kano a yau, wato Ambassador Alhaji Ahmadu Haruna Zago, wanda a fagen siyasar Kano aka fi saninsa da Danzago.

  • Malamai Sun Gargadi Tinubu Kan Daukar Matakin Soji A Kan Nijar
  • Mai Magana Da Yawun Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Yi Karin Haske Kan Bayanan Kafofin Watsa Labarai Game Da Sanarwar Italiya Na Kin Tsawaita Yarjejeniyar Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

Ambassador Danzago, ya yi wata shimfida ne yayin tattaunawar tamu, inda ya faro tun daga Shekarar 1999, lokacin da Engr Rabi’u Musa Kwankwaso ne gwamnan Kano. Har Kwankwason ya bar kujerar mulkin ta Kano, wannan ma’aikata ta shara na amsa sunan REMASAB (Kano State Refuse Management & Sanitation Board) ne. Haka, shi ma Malam Shekarau, tun da yake bisa kujerar gwamnan Kano, daga Shekarar 2003 zuwa 2011, bai canja sunan hukumar ba. Bugu da kari, da Kwankwaso da Shekarau, duka sun yi kokarin samar da kayan aiki ga wannan hukuma ta shara. Sannan, sa’adda maigirma Engr. Dr Rabi’u Musa Kwankwaso ya dawo zangon mulkinsa na biyu a Shekarar 2015,  ya sake gwangwaje wannan hukuma ta Remasab da kayan aiki, irin wadanda ake matukar kishirwarsu a lokacin. Sabbin mabanbantan motoci kar na aikin shara kimanin guda arba’in da biyar (45) ne ya danka su ga hukumar ta Remasab. Sannan, har ya sauka, hukumar na karkashin kulawar gwamnati ne, damfare da sunanta da ta yi shuhura da shi, wato Remasab.

ADVERTISEMENT

Ambassador Danzago ya kara da cewa,  tsohon gwamna Ganduje kuwa, wanda ya dare bisa kujerar gwamnan Kano a Shekarar 2019 zuwa 2023, ya sami hukumar ta Remasab karkashin kulawar gwamnatin Kano ne, amma gabanin saukarsa, sai ya gabatar da wata yarjejeniya tsakanin gwamnati da wani kamfani, ta yadda hukumar za ta tashi karkashin kulawar gwamnati zuwa ga wasu tsirarin mutane. Sai dai, tun kafin a je da nisa, sai wannan yarjejeniya ta ruguje, ko dai saboda wata kuskunda da aka samu ne daga wancan kamfani, ko kuma, watakil gwamnati ba ta tsaya tsai ta nazarci lamarin ba irin yadda ya kamata.

Ko da maigirma gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya sami damar zama za6a66en gwamnan wannan jiha tamu ta Kano, sai ya nuna fa da gaske yake wajen yin duk mai yiwuwa wajen kawar da kazantar sharar da ta yi wa jihar Kano katutu ba tare da yin wata kasa a gwiwa ba, in ji Danzago. Sannan, tsohon sunan da aka san ma’aikatar da shi tun azal, wato Remasab, nan take sabon gwamna ya lashi takobin dawo mata da shi, tare da yin iya iyawarsa wajen dawo da wannan ma’aikata cikin haiyacinta.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

A kan hanyar cika kudirin gwamna na farfado da ran wannan ma’aikata in ji Danzago, shi ma shugaban hukumar sauraren korafe korafen jama’a ta Kano, Muhuyi Magaji R/Gado, ya shiga ya fita, har sai da ya dawowa da wannan hukuma wasu manyan motoci nata guda bakwai (7) da ma wasu, wadanda a baya aka sai da su ba bisa ka’ida ba. Yanzu haka, mun sa motocin na gudanar da aiyukansu a hukumar. Da yawan kayan wannan hukuma da aka sayar, Muhuyin, ya yi azamar dawo mana da su alhamdulillaHi.

Idan ba a manta ba, cikin wata jarida ta yanar gizo da ake kiranta da Dailynigerian.com, an jiyo mai magana da yawun gwamnan Kano, Sanusi Bature D/Tofa na gabatar da wani zargi da ake yi wa tsohuwar gwamnatin Ganduje, na sayar da akasarin manyan kadarorin wannan hukuma ta Remasab,  cikin fakewa da kulla ciniki na hadin gwiwa tsakanin gwamnati da wani kamfani, an sayar da su ne ga iyalai da kuma abokai, inda maigirma gwamnan Kano Abba Kabir ke fassara lamarin da wani abin kaico!.

Haka zalika, za mu yi duk mai yiwuwa, wajen ganin cewa iya wuraren da hukuma ta sahale ne kawai za a zuba shara a wurin. Ko alama, ba za mu lamunci jirkitar da shara barkatai a ko’ina cikin birni da kewaye ba, in ji Danzago.

Danzagon ya ci gaba da cewa,  mu na aiki ne yanzu haka dare da rana ba tare da kakkautawa ba. Dole ne shugaba ya fita, ba ya makale cikin ofis ba, ba tare da sanin abinda ke faruwa a waje ba. Shi shugaba, shi ne mai yi wa mutane hidima a ko da yaushe. Shi yasa lokacin da muka shiga aiki can “Yan dabino Yakasai lokacin da ake lafta mamakon ruwa, sai jama’ar unguwar suka rika mamakinmu. Ba wannan ma’aikata tawa ta Remasab ba kawai, kusan kowace ma’aikata na bisa sirdin aiwatar da aiyuka ne, duba da kalaman gwamna cewa, zuwa Watanni shida, duk wani da aka nada bisa wata kujera sai bai yi abin kirki ba, a fili ne yake cewa wannan mutumi ya sallami kansa da kansa.

Ambassador Danzago ya kara da cewa, yanzu haka suna nan suna tantance hakikanin ma’aikatansu a takarda, kuma za su bi su har wuraren da suke aiki don tabbatarwa. Bugu da kari, duk wani ma’aikacinmu da ke da wani hakki na gaskiya, a shirye muke da mu ba shi hakkin nasa.

Babu shakka, muddin kowace ma’aikata za ta tashi haikan wajen sauke nauyin da maigirma gwamna Abba Kabir Yusuf ya aza mata, la-budda za a haife da-mai-ido a Kano.

Kano
Muhammad Awwal Umar
+ postsBio
  • Muhammad Awwal Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-awwal-umar/
    Yadda Mayar Da Gonaki Fulotai Ke Tsananta Karancin Abinci
  • Muhammad Awwal Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-awwal-umar/
    Gwamnatoci Sun Fara Daukar Matakan Dakile Yunwa
  • Muhammad Awwal Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-awwal-umar/
    Neja Za Ta Gyara Makarantun Rugagen Fulani
  • Muhammad Awwal Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-awwal-umar/
    Ba Mu Hana Sulhu Da ‘Yan Ta’adda Ba, Amma A Bar Jami’an Tsaro Su Yi Aikinsu – Bosso

MASU ALAKA

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna
Rahotonni

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

July 18, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu
Rahotonni

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau
Rahotonni

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Next Post
Manchester United Za Ta Bayyana Matsayarta A Kan Greenwood

Manchester United Za Ta Bayyana Matsayarta A Kan Greenwood

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao

Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao

July 21, 2026
An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026

An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026

July 21, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

July 21, 2026
Li Qiang Ya Taya Andy Burnham Murnar Zama Sabon Firaministan Birtaniya

Li Qiang Ya Taya Andy Burnham Murnar Zama Sabon Firaministan Birtaniya

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida

Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida

July 21, 2026
Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule

Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Bayar Da Tallafin Sama Da Ton 3,000 Na Abinci Ga Sudan Ta Kudu

Kasar Sin Ta Bayar Da Tallafin Sama Da Ton 3,000 Na Abinci Ga Sudan Ta Kudu

July 21, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Harbe Mai Unguwa Har Lahira A Bauchi

July 21, 2026
Sojoji Sun Daƙile Shirin Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Wadanda Aka Sace A Zamfara Da Katsina

Sojoji Sun Daƙile Shirin Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Wadanda Aka Sace A Zamfara Da Katsina

July 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.