• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Ci Gaba Da Daukar Shirin ‘The Mandate’ A Kasar Faransa – Ezinne Agwu

by Sulaiman and Rabilu Sanusi Bena
1 year ago
in Nishadi
0
mandate
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masana’antar Nollywood tana gab da shaida wani gagarumin ci gaba, a yayin da Dakta Princess Ezinne Agwu, sabuwar mai shirya fina-finai a masana’antar Nollywood, ta kammala shirin fim na farko na miliyoyin nairori mai suna, “The Mandate,” a birnin Paris na kasar Faransa.

Dakta Ezinne, wacce ta canza sana’a daga mai shari’a ta kasa da kasa zuwa harkar fim, ta hada kai da fitaccen daraktan Nollywood, Ike Nnaebue domin kawo wannan wasan kwaikwayo a idon duniya.

  • Lamunin Naira Biliyan 5 Ga ‘Yan Fim: Yaushe Kannywood Za Ta Samu Nata?
  • Ali Nuhu Ya Gabatar Da Lacca Kan Fina-finan Nijeriya A Faransa

Ike Nnaebue, wanda ya dawo harkar fina-finai na barkwanci bayan nasarar shirinsa na “No U-Turn,” shi ne darakta a wannan shiri wanda ake fatan idan an kammala shi ya zama irinsa na farko da wani dan Nijeriya ya taba shiryawa. Wannan fim din ya janyo wa Dakta Ezinne yabo mai yawa da suka hada da jinjinan ‘Jury Berlinale’ da kyaututtuka daga kwalejin fina-finan Afirka da bikin fina-finai na duniya na Durban.

Da yake magana game da fin din “The Mandate” da hadin gwiwarsa tare da Dakta Ezinne, Ike ya ce wannan buri ne na kowane mai shirya fina-finai, domin yin aiki mai nagarta tare da samar da fasaha mai muhimmanci.

Ya ce fim din “The Mandate” labari ne na jarumtaka a cikin duniyar da tsoro ya zama aikin yau da kullun.

Labarai Masu Nasaba

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

Majiyoyin da ke kusa da ‘Royalty Life Studios’, inda Dakta Ezinne ke aiki a matsayin shugaba, sun nuna cewa kasafin kudin fim din ya wuce naira miliyan 700.  Sai dai Dakta Ezinne ta ki tabbatar da ainihin alkaluman, inda ta ce, “Ba a gama fim din ba tukuna, za mu bayyana kasafin kudin fim din idan an kamala shi.

Labarin fim din ya nuna yadda Dakta Ezinne Egbuna, Darakta-Janar na Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa, wanda ke kalubalantar halin da ake ciki a fagen siyasar Nijeriya da maza suka mamaye.

A yunkurinta na yaki da cin hanci da rashawa da bunkasar ci gaba, ta yi murabus daga mukaminta mai daraja ta tsaya takarar gwamna a karkashin jam’iyyar DPC, karkashin jagorancin Hon.  Lucas Amadi, wanda yake fuskantar adawa mai zafi daga DPA da makiya na boye a cikin jam’iyyar tasa.

Fim din ya kunshi fitattun jaruman da suka hada da Femi Adebayo, Deyemi Okanlawon, Ali Nuhu, Kalu Ikeagwu, Okey Bakasi, Sarauniya Dimma Edochie, Chioma Nwoha da kuma gabatar da sabon jarumi, Peter Ngene.

Dakta Ezinne ta jaddada cewa shawarar da aka yanke na gudanar da ayyukan bayan fage a birnin Paris ya yi daidai da hangen nesanta na samar da labarun gida tare da jawo hankalin duniya.

Ta ce, “Mun himmatu wajen bayar da labarun gida ga masu sauraron duniya,” in ji ta.

Yayin wani taron manema labarai a Abuja za a sanar da cikakkun bayanai kan shirin fitar da fim din da kwanan wata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Lokaci Ya Yi Da Nijeriya Za Rika Fitar Da Manja Kasashen Waje – Kungiyar Dalibai

Next Post

Sabbin Naɗe-Naɗe 10 Da Shugaba Tinubu Ya Yi Jiya

Related

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah
Nishadi

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

18 hours ago
Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya
Nishadi

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

1 week ago
Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu
Nishadi

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

2 weeks ago
Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya
Nishadi

Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

2 weeks ago
An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna
Nishadi

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

2 weeks ago
Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ
Nishadi

Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

3 weeks ago
Next Post
Sabbin Naɗe-Naɗe 10 Da Shugaba Tinubu Ya Yi Jiya

Sabbin Naɗe-Naɗe 10 Da Shugaba Tinubu Ya Yi Jiya

LABARAI MASU NASABA

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.