• English
  • Business News
Monday, July 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Ceto Zamfara, In Ji Atiku Yayin Da Ya Amshi Baƙuncin Dauda Lawal

by Bello Hamza
3 years ago
in Siyasa
0
Za Mu Ceto Zamfara, In Ji Atiku Yayin Da Ya Amshi Baƙuncin Dauda Lawal
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ɗan takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam’iyyar PDP kuma tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar ya jaddadawa Ɗan takarar gwamnan Jihar Zamfara, Dr. Dauda Lawal cewa zai yi aiki tuƙuru wurin ganin jam’iyyar PDP ta lashe zaɓen 2023 a Jihar da ma ƙasa bakidaya.

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasan ya bayyana haka ne jiya laraba a gidansa dake Abuja, yayin da Dauda Lawal ya jagoranci tawagar ‘ya’yan PDP na Jihar Zamfara tare da wasu jiga-jigan ‘yan siyasa da suka sauka sheƙa daga APC zuwa PDP.

  • Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Yanke Wa Abdulmalik Tanko Hukuncin Kisa

Atiku ya ce, hanya daya ce za a iya bi wurin ceto Zamfara, shi ne ta hanyar korar APC daga mulki.
“Ba za mu samar da nagartacciyar rayuwa ga jama’a ba har sai mun tabbata mun kori APC, wanda kuma hakan na buƙatan hadin kai.
“Babban abin da mutanen Zamfara ke buƙata a yanzu shi ne zaman lafiya. A samar da tsaro a gonaki, a samar da ayyukan yi. Idan aka yi haka, za a samu inganci a komi na rayuwa” Inji shi

Tun farko a jawabinsa, dan takarar gwamna na PDP a Zamfara, Dr. Dauda Lawal ya bayyana dalilin wannan ziyara a matsayin gaisuwa tare da gabatar da jiga-jigan ‘yan siyasar da suka sauya sheƙa daga APC zuwa PDP. Haka nan kuma don taya murna ga Atiku bisa nasarar da ya samu a zaben fidda gwanin PDP wanda aka yi kwanakin baya.

Lawal ya ce, ‘yan Nijeriya sun gaji da APC, a shirye suke da su zabi PDP a matakin jihohi da ma tarayya. “Samun waɗannan manyan ‘yan siyasa su sauya sheka daga APC zuwa garemu, ba ƙaramar nasara ba ce ga PDP”. Inji shi.

Labarai Masu Nasaba

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

Daga cikin jiga-jigan da suka sauya shekan daga APC zuwa PDP akwai Alhaji Salihu Mai Buhu Gummi, Alhaji Sahabi Liman Kaura, Alhaji Illili Bakura, Engr. Garba Ahmad Yandi, Hon. Ikra Bilbis, Dr. Na’Allah Isa Mayana, Hon. Mukhtar Lugga da sauransu.

Kafin kammala ziyarar, Dauda Lawal ya gabatarwa da Atiku da kyautar rigar saka a matsayin ɗaya daga cikin abubuwan da Zamfara ta shahara da su a baya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Yanke Wa Abdulmalik Tanko Hukuncin Kisa

Next Post

Tinubu Bai Cancanci Zama Shugaban Kasa Ba, Ya Tsufa, Cewar Surukinsa Tee Mac

Related

Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

1 day ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

3 days ago
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista
Manyan Labarai

Shugabannin Jam’iyyar ADC Na Jihohi 36 Da Abuja Sun Bayyana Goyon Bayansu Ga David Mark

3 days ago
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta
Labarai

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

4 days ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Siyasa

Babu Wanda Ya Buƙaci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC

5 days ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027

7 days ago
Next Post
Tinubu Bai Cancanci Zama Shugaban Kasa Ba, Ya Tsufa, Cewar Surukinsa Tee Mac

Tinubu Bai Cancanci Zama Shugaban Kasa Ba, Ya Tsufa, Cewar Surukinsa Tee Mac

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Na Kokarin Tabbatar Da Ci Gaban Da Aka Samu Na Yarjejeniyar London

Sin Da Amurka Na Kokarin Tabbatar Da Ci Gaban Da Aka Samu Na Yarjejeniyar London

July 14, 2025
Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

July 14, 2025
Sin Na Maraba Da ’Yan Jaridar Duniya Da Su Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Harin Japan Da Na Tafarkin Murdiya 

Sin Na Maraba Da ’Yan Jaridar Duniya Da Su Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Harin Japan Da Na Tafarkin Murdiya 

July 14, 2025
Osimhen Na Dab Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Osimhen Na Dab Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 14, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

July 14, 2025
Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami

Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami

July 14, 2025
Cinikayyar Shige Da Fice Ta Sin Ta Karu Da Kaso 2.9 Bisa Dari A Watanni Shida Na Farkon Bana

Cinikayyar Shige Da Fice Ta Sin Ta Karu Da Kaso 2.9 Bisa Dari A Watanni Shida Na Farkon Bana

July 14, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni

July 14, 2025
Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari

Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari

July 14, 2025
Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Tsara Yadda Za A Binne Buhari

Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Tsara Yadda Za A Binne Buhari

July 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.