• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Tabbatar Da Nasarar Tsarin Ba Da Inshorar Kiwon Lafiya A Kebbi – Dakta Augie

by Umar Faruk
3 years ago
Augie

Hukumar kula da Inshorar kiwon lafiya ta jihar Kebbi (KECHEMA) ta dorawa kungiyoyin farar hula, kungiyoyin kwadago, kwararrun ma’aikatan lafiya da kuma kafafen yada labarai aikin bayar da shawarwari da yada labarai ga jama’a kan shirin Inshorar kiwon lafiya na hukumar a jihar.

 

Sakataren zartarwa na hukumar Dakta Jafar Augie ne ya bukaci hakan a wajen bikin rufe taron na kwanaki biyu da aka gudanar a Sukura Otal da ke jihar Sakkwato wanda aka shirya tare da hadin gwiwar hukumar lafiya ta Integrated Health Programme (IHP).

  • Buhari Ya Yi Jajen Hatsarin Jirgin Ruwa A Kebbi

Ya ce, “Shirin na mu ne a matsayinmu na ’yan uwa da masu ruwa da tsaki a lokaci guda; ba na gwamnati ba ne, don haka ya rage gare mu na tabbatar da tsarin ya samun nasara ko akasin haka,’ Inji shi.

 

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

“Ya kamata mu rungumi tsarin mu mallake shi kamar yadda gwamnati ta yi aikinta ta hanyar ba wa tsarin doka da ka’idojin gudanar da aiki da kuma wuraren da suka dace.

 

“Babu abinci kyauta yanzu a duniya; dole ne mu ba da gudummawa don haɓaka ingantaccen isar da lafiya. Allah zai iya kalubalance mu idan muka zabi rashin tausayin jama’amu ga kula da kiwon lafiya,” inji shi.

 

Augie ya bukaci masu ruwa da tsaki da su tabbatar da dorewar da kuma tsayuwar tsarin Inshorar kiwon lafiya wajen samar da kudaden da za su bayar da gudummuwar cin nasarar tsarin, yana mai cewa alhakin ya rataya ne a kan dukkan masu ruwa da tsaki.

 

A cewarsa, hukumar na da hurumin tabbatar da ingantacciyar hidimar kiwon lafiya ga kowa da kowa a jihar.

 

Haka zalika Dokta Augie ya yaba wa mahalarta taron, wadanda ya bayyana a matsayin, dukkan muhimman membobi na kungiyar aiki na fasaha kuma sun ba da himma wajen tsara tsarin.

 

“Za mu ci gaba da kasancewa masu godiya. Muna matukar godiya ga abokan aikinmu na ci gaba, USAID da hukumominta masu ba da tallafi ga kiwon lafiya da gudanar da mulki da Integrated Health Project (IHP) da sauransu,” in ji sakataren.

 

A nata bangaren, mai ba da shawara kan harkokin kudade da kasafi na IHP, Dakta Aisha Aminu-Senchi, ta bayyana cewa, IHP na hada kai da gwamnatocin jihohi wajen karfafawa da kuma ciyar da ayyukan inshorar lafiya na jihohi gaba, domin cimma burin samar da kiwon lafiya na duniya baki daya.

 

Ta bayyana cewa talakawan kasa ba za su iya biyan kudaden da samar da Inshorar lafiyar kansu ba, tana mai cewa ya kamata ’yan kasa masu wadata da su rika biyama wadanda ba su don amfani da kuma masu karamin karfi don iya dogaro da kai.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100
Labarai

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato
Manyan Labarai

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi
Labarai

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Next Post
Gwamnan Gombe Ya Bada Tallafin Miliyan 25 Ga Ƙungiyar CAN Don Gina Masaukin Baki

Gwamnan Gombe Ya Bada Tallafin Miliyan 25 Ga Ƙungiyar CAN Don Gina Masaukin Baki

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
Augie

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.