• English
  • Business News
Friday, August 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Tabbatar Da Nasarar Tsarin Ba Da Inshorar Kiwon Lafiya A Kebbi – Dakta Augie

by Umar Faruk
3 years ago
in Labarai
0
Za Mu Tabbatar Da Nasarar Tsarin Ba Da Inshorar Kiwon Lafiya A Kebbi – Dakta Augie
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar kula da Inshorar kiwon lafiya ta jihar Kebbi (KECHEMA) ta dorawa kungiyoyin farar hula, kungiyoyin kwadago, kwararrun ma’aikatan lafiya da kuma kafafen yada labarai aikin bayar da shawarwari da yada labarai ga jama’a kan shirin Inshorar kiwon lafiya na hukumar a jihar.

 

Sakataren zartarwa na hukumar Dakta Jafar Augie ne ya bukaci hakan a wajen bikin rufe taron na kwanaki biyu da aka gudanar a Sukura Otal da ke jihar Sakkwato wanda aka shirya tare da hadin gwiwar hukumar lafiya ta Integrated Health Programme (IHP).

  • Buhari Ya Yi Jajen Hatsarin Jirgin Ruwa A Kebbi

Ya ce, “Shirin na mu ne a matsayinmu na ’yan uwa da masu ruwa da tsaki a lokaci guda; ba na gwamnati ba ne, don haka ya rage gare mu na tabbatar da tsarin ya samun nasara ko akasin haka,’ Inji shi.

 

Labarai Masu Nasaba

Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa

Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara

“Ya kamata mu rungumi tsarin mu mallake shi kamar yadda gwamnati ta yi aikinta ta hanyar ba wa tsarin doka da ka’idojin gudanar da aiki da kuma wuraren da suka dace.

 

“Babu abinci kyauta yanzu a duniya; dole ne mu ba da gudummawa don haɓaka ingantaccen isar da lafiya. Allah zai iya kalubalance mu idan muka zabi rashin tausayin jama’amu ga kula da kiwon lafiya,” inji shi.

 

Augie ya bukaci masu ruwa da tsaki da su tabbatar da dorewar da kuma tsayuwar tsarin Inshorar kiwon lafiya wajen samar da kudaden da za su bayar da gudummuwar cin nasarar tsarin, yana mai cewa alhakin ya rataya ne a kan dukkan masu ruwa da tsaki.

 

A cewarsa, hukumar na da hurumin tabbatar da ingantacciyar hidimar kiwon lafiya ga kowa da kowa a jihar.

 

Haka zalika Dokta Augie ya yaba wa mahalarta taron, wadanda ya bayyana a matsayin, dukkan muhimman membobi na kungiyar aiki na fasaha kuma sun ba da himma wajen tsara tsarin.

 

“Za mu ci gaba da kasancewa masu godiya. Muna matukar godiya ga abokan aikinmu na ci gaba, USAID da hukumominta masu ba da tallafi ga kiwon lafiya da gudanar da mulki da Integrated Health Project (IHP) da sauransu,” in ji sakataren.

 

A nata bangaren, mai ba da shawara kan harkokin kudade da kasafi na IHP, Dakta Aisha Aminu-Senchi, ta bayyana cewa, IHP na hada kai da gwamnatocin jihohi wajen karfafawa da kuma ciyar da ayyukan inshorar lafiya na jihohi gaba, domin cimma burin samar da kiwon lafiya na duniya baki daya.

 

Ta bayyana cewa talakawan kasa ba za su iya biyan kudaden da samar da Inshorar lafiyar kansu ba, tana mai cewa ya kamata ’yan kasa masu wadata da su rika biyama wadanda ba su don amfani da kuma masu karamin karfi don iya dogaro da kai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sinawa ‘Yan Sama Jannati Sun Gabatar Da Gaisuwar Sabuwar Shekara Daga Cibiyar Binciken Sararin Samaniya

Next Post

Gwamnan Gombe Ya Bada Tallafin Miliyan 25 Ga Ƙungiyar CAN Don Gina Masaukin Baki

Related

Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa
Manyan Labarai

Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa

29 minutes ago
Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara
Manyan Labarai

Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara

1 hour ago
Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare
Labarai

Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

9 hours ago
NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata
Labarai

NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata

9 hours ago
Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe
Labarai

Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe

10 hours ago
Gwamnati Na Ƙoƙarin Tsoratar Da Ni Don In Shiga APC – Sanata Tambuwal
Labarai

Gwamnati Na Ƙoƙarin Tsoratar Da Ni Don In Shiga APC – Sanata Tambuwal

11 hours ago
Next Post
Gwamnan Gombe Ya Bada Tallafin Miliyan 25 Ga Ƙungiyar CAN Don Gina Masaukin Baki

Gwamnan Gombe Ya Bada Tallafin Miliyan 25 Ga Ƙungiyar CAN Don Gina Masaukin Baki

LABARAI MASU NASABA

Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa

Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa

August 15, 2025
Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara

Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara

August 15, 2025
Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

August 14, 2025
NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata

NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata

August 14, 2025
Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana

Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana

August 14, 2025
Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe

Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe

August 14, 2025
Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

August 14, 2025
Gwamnati Na Ƙoƙarin Tsoratar Da Ni Don In Shiga APC – Sanata Tambuwal

Gwamnati Na Ƙoƙarin Tsoratar Da Ni Don In Shiga APC – Sanata Tambuwal

August 14, 2025
Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Masana’antar Lantarki Ya Ci Gaba Da Samun Karfin Juriya A Kasar Sin

Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Masana’antar Lantarki Ya Ci Gaba Da Samun Karfin Juriya A Kasar Sin

August 14, 2025
Gidauniya Ta Rabar Da Buhun Takin Zamani 6,000 Ga Manoma A Bauchi 

Gidauniya Ta Rabar Da Buhun Takin Zamani 6,000 Ga Manoma A Bauchi 

August 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.