Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home RAHOTANNI

Za Mu Yi Saukar Alkur’ani 1,111 Domin Zaman Lafiya A Kasa – Gwani Aliyu Turaki

by Muhammad
April 6, 2021
in RAHOTANNI
1 min read
Za Mu Yi Saukar Alkur’ani 1,111 Domin Zaman Lafiya A Kasa – Gwani Aliyu Turaki
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abdullahi Muhammad Sheka,

Shugaban Majalisar Mahaddata Alkaur’ani na kasa, Gwani Aliyu Salihu Turaki, babban limamin Masallachin Juma’a na Alhassan dantata dake Kano, ya bayyana aniyar majalisar ta gudanar da saukokin Alkur’ani mai girma 1,111 a kowacce jiha domin rokon Allah ya kawo karshen barazanar matsalar tsaro da ke addabar kasarnan.

Shugaban na wannan jawabi ne jim kadan da kammala saukokin Alkur’ani 1,333 wanda aka gudanar a Masallachin juma’a na Shiekh Muhammadu Rabiu dake Goron Dutse a Jihar Kano ranar litinin data Gabata. Kamar yadda aka saba, wannan na cikin kokarin marigayi Khalifa Sheikh Isyaka Rabiu Allah ya jikansa da gafara ke kokarin shiryawa wanda ya kira da ranar wannan taro da Yaumul-kur’an.

Gwani Aliyu Salihu Turaki ya bayyana cewa, babu wata mafita ga halin da ake ciki illa rungumar addu’o’i tare da yin tawassili da Alkur’ani domin rokon Allah kan halin da al’umma ke ciki. Saboda haka sai Shugaban ya bukaci shugabannin wannan Majalisa mai albarka na jihohin kasarnan da kowa ya shirya irin wannan taron addu’ar domin taimakawa aniyar Gwamnati na magance matsalar tsaro a fadin kasarnan.

Haka zalika Shugaban ya isar da Sakon bangajiya ga Alarammomi 1,111 da Suka halarci taron bana da aka gudanar a Gusau babban burnin Jihar Zamfara. Daga nan sai ya jinjinawa kokarin Gwamnatin Jihar Zamfara karkashin jagorancin Gwamna Dr. Bello Muhammad Matawalle bisa hidimar da ya yiwa ahlullahi alokacin taron, ya yi addu’ar fatan Allah ya kawowa kasarnan karshen matsalar tsaro dake addabar kasarnan baki daya.

Taron na Yaumul-kur’an ya samu halartar Alarammomi daga kananan Hukumomin Jihar Kano 44, sai Kuma wakilin al’ummar karamar Hukumar birni dabkewaye Hon. Sha’aban Ibrahim Sharada, khalifa Alhaji Nafi’u Isyaka Rabiu da sauran manyan baki.

SendShareTweetShare
Previous Post

Gina Gadojin Sama: Ko Gasa Gwamnonin Jihohin Arewa Ke Yi?  

Next Post

An Yaba Wa Gwamnatin Kaduna Kan Samar Da Cibiyoyin Warkar Da ‘Yan Kwaya

RelatedPosts

Babandede Ya Yi Gargadi A Kan Daukan Aiki Na Bogi Da Sunan NIS

Sauye-sauye Masu Ma’ana A Sashen Fasfo Na Hukumar Shige Da Ficen Nijeriya

by Yahuzajere
5 hours ago
0

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Nijeriya (NIS), karkashin...

An Gabatar Da Huduba Kan Ramadan A Babban Masallacin Jos

An Gabatar Da Huduba Kan Ramadan A Babban Masallacin Jos

by Sulaiman Ibrahim
6 hours ago
0

Daga Mohammed Ahmed Baba, Jos A ranar Juma'ar nan ne...

Yadda Tu’amalli Da Kayan Maye Ke Shafar Lafiyar Matasa Maza Da Mata  – Margaret

Yadda Tu’amalli Da Kayan Maye Ke Shafar Lafiyar Matasa Maza Da Mata  – Margaret

by Sulaiman Ibrahim
6 hours ago
0

Uwargida  Margaret  Juliu, sananniyar ce a jihar Kaduna,  musamman wajen fadakar...

Next Post
An Yaba Wa Gwamnatin Kaduna Kan Samar Da Cibiyoyin Warkar Da ‘Yan Kwaya

An Yaba Wa Gwamnatin Kaduna Kan Samar Da Cibiyoyin Warkar Da ‘Yan Kwaya

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version