• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben 2023: Gwamnoni Masu Barin Gado Da Suka Fadi Zaben Kujerar Sanata 

by Abubakar Abba
3 years ago
Zaben 2023

Akalla gwamnoni shida masu barin gado ne a fadin kasar nan suka gaza kai bantensu bayan tsayawa takarar kujerar Sanata a mazabunsu.

Gwanonin wadanda suka yi wa’adin shekara takwas a kan kujerunsu, sun sha kasa ne a zabukan Sanatan da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabirairu 2023.

  • Da Dumi-Dumi: PDP, LP Da ADC Dun Bukaci INEC Ta Gudanar Da Sabon Zabe
  • Peter Obi Ya Lashe Birnin Tarayya

Tun bayan dawowar mulkin dimokuradiyya a 1999, an danganta majalisar wakilai da kuma ta dattijai a matsayin wata mafakar tsofaffin gwamnoni.

Kimanin tsofaffin gwamnoni 20 aka zaba zuwa ga majalisa ta tara a 2019.

Tsofaffin gwanonin da a yanzu ke majalisar dattawa su ne, Rochas Okorocha daga Jihar Imo, Ibikunle Amosun daga Jihar Ogun, Abdulaziz Yari daga Jihar Zamfara Kabiru Gaya daga Jihar Kano, Abdullahi Adamu daga Jihar Nasarawa, Chimaroke Nnamani daga Jihar Enugu, Kalu daga Jihar Abia, Gabriel Suswam daga Jihar Binuwe da kuma Ibrahim Shekarau daga Jihar Kano da sauransu.

LABARAI MASU NASABA

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Wadanda a bana suka shiga zaben sun hada da, gwamnan Jihar Ebonyi David Umahi, gwamnan Jihar Neja Abubakar Bello da kuma gwamnan Abia Okezie Ikpeazu wadanda suka lashe zaben na ranar asabar.

Sai dai, Atiku Bagudu na Jihar Kebbi ya fadi yayin da ba a bayyana na gwaman Sakkwato Aminu Tambuwal ba.

Tsofaffin gwanonin da suka lashe zaben Sanata su ne, Adams Oshiomhole daga Jihar Edo sai kuma tsohon gwamnan Akwa Ibom Godswill Akpabio.

Ga jerin sunayen gwamonin masu barin gado da suka gaza lashe zaben bayan sun kammala wa’adin mulkinsu a watan Mayu 29, 2023.

Dan takarar Sanata na APC Titus Zam ya kayar da Samuel Ortom gwaman Jihar Binuwe a zaben Sanata na mazabar Binuwe ta Arewa Maso Gabas, inda Zam ya samu kuri’u 143,151, Ortum gwannan PDP na G-5, ya samu kuri’u 106,882, sai LP ta samu kuri’u 51,950.

Gwamna Ifeanyi Ugwuanyi ya gaza lashe zaben Sanata na mazabar Enugu ta Gabas.

Dan takarar Sanata a LP Okechukwu Ezea ne INEC ta sanar ya lashe zaben, inda ya samu kuri’u 104,948, Ugwuanyi kuma ya samu kuri’u 46,948.

Akwai kuma gwamnan Jihar Taraba Darius Ishaku wanda ya sha kasa a zaben mazabar Taraba ta Kudu, inda dan takara David Jimkuta, daga APC ya kayar da shi bayan ya samu kuri’u 85,415 Ishaku kuma ya samu kuri’u 45,708.

Gwamnan Jihar Filato Simon Lalong kuma darakta-janar na kwamitin yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC kuma shugaban kungiyar Gwamnonin Arewa, dan takarar Sanata a PDP Bali Ninkap Napoleon ya kayar da shi bayan ya samu kuri’u 148,844 inda Lalong ya samu kuri’u 91,674.

Gwannan Jihar Koros Ribas Ben Ayade ya sha kasa a hannun Jarigbe Agom-Jarigbe dan takarar Sanata a jam’iyyar PDP, wanda dama can shi ne yake a kan kujerar, inda Agom ya samu kuri’u 76,145 sai kuma Ayade ya samu kuri’u 56,595.

Ayade kafin a zabe shi gwamna, ya kasance zababben Sanata ne daga

2011 zuwa 2015, inda a zaben 2023, ya so ya sake komawa majalisar dattawa

don ya wakilci mazabar Koros Ribas ta Arewa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai
Manyan Labarai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya
Manyan Labarai

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Next Post
Sin Za Ta Ba Da Gudummawa Wajen Tafyar Da Harkokin Hakkin Dan Adam A Duniya

Sin Za Ta Ba Da Gudummawa Wajen Tafyar Da Harkokin Hakkin Dan Adam A Duniya

LABARAI MASU NASABA

…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025
CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

November 5, 2025
Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.