• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben 2023: Na’urar BVAS Ta Ki Tantance Yakubu Dogara

by Khalid Idris Doya
3 years ago
BVAS

Na’urar tantance masu zabe wato BVAS, ta gaza daukan zanen yatsu da hoton fuskar tsohon kakakin Majalisar Dokokin Tarayya, Hon. Yakubu Dogara.

Dogara wanda ya je rumfar zabensa da ke Kauyen Kwarangah da ke karamar hukumar Bogoro a rumfar mai lamba 007 tun wajen 10 na safiya har zuwa 2:pm amma na’urar ta kasa tantance shi balle ya samu damar jefa kuri’arsa.

  • PDP Za Ta Kai Ga Nasara -Tambuwal
  • Ina Da Kwarin Guiwar Lashe Zabe -Tinubu

Lamarin dai ya sanya shi zaman dirshen kawai a wajen zaben da jiran ko na’urar za ta sahaleshi.

Da ya ke zantawa da ‘yan jarida kan wannan matakin, Yakubu Dogara ya nuja takaicinsa na cewa na’urar BVAS guda daya tak ke aiki a mazabar duk da cewa masu zabe sun kusan kaiwa mutum 2,000 a wajen.

Kazalika ya shaida cewar wasu ma da dama na’urar ta kasa tantance su don haka ya yi zargin cewa ana shirin fusata jama’a har su koma gidajensu ba tare da yin zaben ba.

LABARAI MASU NASABA

Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur Ba – Sanusi II

Atiku Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Sauya Sunayen Waɗanda Aka Yi Wa Afuwa

Dogara ya ce, lokacin da ya zo na’urar ba ta tantance shi ba, ya garzaya ofishin INEC da ke karamar hukumar Bogoro domin neman bahasin yadda aka dauki BVAS din Kwaranga zuwa karamar hukumar Tafawa Balewa.

Ya nuna takaicinsa kan yadda al’umma suka bar gidajensu suka fito domin kada kuri’a amma na’urar ta ki tantance su, “Ana ta kan ba da hakuri wa jama’a, to amma muna ganin takaici ne, an ce mana BVAS machine din nan da aka ce ko ma ina ko inda babu network zai yi aiki. Yanzu mun zo an ce ba ta aiki, an dauka an kai Tafawa Balewa, gari da ke da nisan kilomita 12 zuwa 13 daga inda muke a yau don a je a samu network.

“Amma abun da za a lura da shi a nan kasar Kwarangah akwai network masu karfi guda biyu na MTN da Glo. Damuwar mu shi ne meye sa za a dauki BVAS na Kwarangah a kai shi Tafawa Balewa domin a gyara, ko ma network din bai da karfi ai akwai network a Bogoro.

Ya ce, baya ga wannan duk rumfar jefa kuri’ar da ke masu zabe sama da dubu biyu ya kamata a basu BVAS guda hudu, “Amma sun kawo biyu kacal nan duk da masu zabenmu sun kusan dubu biyu. A cikin biyun da suka kawo ma 1 baya aiki. Don haka muna ganin wannan kamar ana son a kular da mutane ne su yi fushi su koma gidaje su ce ba za su yi zabe ba.”

Ya ce za su cigaba da jiran abubuwan da jami’an INEC za su yi domin su na son kada kuri’arsu.

Ya nuna takaicinsa kan yadda na’urar ke cigaba da haifar da koma baya ga zaben.

Daga bisani Dogara ya yi amfani da damar wajen neman jama’a da su yi zabe cikin kwanciyar hankali kuma ya nemi masu takara da su dauki aniyar amsar sakamakon zaben da za a bayyana.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

BVAS
Manyan Labarai

Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur Ba – Sanusi II

October 30, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Sauya Sunayen Waɗanda Aka Yi Wa Afuwa

October 30, 2025
Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci
Manyan Labarai

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

October 29, 2025
Next Post
Faduwar Farashin Kaudar Tumatir Zai Rage Wa Manoma Karfin Gwiwa

Faduwar Farashin Kaudar Tumatir Zai Rage Wa Manoma Karfin Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

BVAS

Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur Ba – Sanusi II

October 30, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Sauya Sunayen Waɗanda Aka Yi Wa Afuwa

October 30, 2025
Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Asuu

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025
Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

October 29, 2025
Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

October 29, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

October 29, 2025
Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.