• English
  • Business News
Tuesday, September 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben 2023: PDP Ta Gargadi Tinubu Kan Ikirarin Nasara Bayan Gwamnonin Arewa Sun Gaza Ceto Shi

by Muhammad
3 years ago
in Siyasa
0
Zaben 2023: PDP Ta Gargadi Tinubu Kan Ikirarin Nasara Bayan Gwamnonin Arewa Sun Gaza Ceto Shi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa a jam’iyyar PDP, ta gargadi dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu, da kada ya ba kansa nasara a zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya na shekarar 2023, yana mai cewa gwamnonin Arewa da yake sa ran za su ba ba shi kuri’u sun gaza sosai.

Kwamitin ya kuma bukaci shugaban kasa, Muhammadu Buhari, da ya ja kunnen Tinubu kan yin ikirarin nasara a zaben na 2023.

  • INEC Ta Dage Zaben Shugaban Kasa Da Na ‘Yan Majalisun Tarayya Zuwa Yau Lahadi A Yenagoa
  • Atiku Ya Lashe Rumfar Zaben Mataimakin Peter Obi, Datti Baba-Ahmed

Kwamitin kamfen din ya bayyana hakan lokacin da yake mayar da martani ga wata kafar yada labarai da ta buga wanda PDP ta ce mallakin Tinubu ne.

Kafofin yada labaran sun yi ikirarin cewa Tinubu ne ke kan gaba a shiyyar Arewa maso Yamma da Kudu maso Yamma da kuma Arewa ta Tsakiya na kasa.

Sai dai Daraktan Sadarwar da Dabaru na
Kwamitin yakin neman zaben Atiku/Okowa, Cif Dele Momodu, wanda ya sanya hannu a wata sanarwa a ranar Lahadi, ya ce Tinubu ne kadai dan takara daya tilo da jam’iyyun adawa suka lalata yankinsa na Kudu maso Yamma a jihohin Legas, Ogun, Ondo, Oyo, Osun da Ekiti.

Labarai Masu Nasaba

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Ya ce, “Dazun nan hankalinmu ya karkata ga labarin da jaridar ta buga mai hatsarin gaske da ke bayar da nasara ga dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu. Jaridar da aka ce mallakin Tinubu ce.

“A jiya ne muka ga yadda ’yan barandar APC da mutanensu suka mamaye titunan Legas suna kona akwatunan zabe da takardu da kuma nuna rashin da’a.

Duk da yunƙuri na satar nasara, APC ta yi asarar mafi muni a mafi yawan wuraren zaɓe a Legas. Haka ya faru a Kano.

A safiyar yau mun wayi gari mun karanta labarin karya da karyar da jaridar Tinubu suka buga.

“Tinubu ya dan takara ne daya tilo da jam’iyyun adawa suka lalata masa Kudu maso Yamma a Legas, Ogun, Ondo, Oyo, Osun da Ekiti. Yawancin Gwamnonin Arewa da ya sa ran za su taimaka masa wajen samun kuri’u a yankunan Arewa sun kasa kai wa ga kuri’un da ake bukata. Ya gaza a Kudu maso Gabas da Kudu Kudu.

“Dan takara daya tilo a kasa shi ne dan takarar shugaban kasa na PDP, tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, a matsayinsa na dan kasa mai kishin kasa, ba zai taba yin gaggawar shiga kafafen yada labarai don neman nasara.” cewarsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AtikuPDPTunibuZaben 2023
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaben 2023: INEC Za Ta Fara Bayyana Sakamakon Zaben Shugaban Kasa

Next Post

Zaben 2023: INEC Ta Dage Bayyana Sakamakon Zaben Shugaban Kasa Zuwa Karfe 6 Na Yamma

Related

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa
Siyasa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

2 days ago
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC
Siyasa

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

3 days ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Siyasa

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Sake Lashe Zaɓe A 2027 – Jigon APC

6 days ago
2027: Fastocin Takarar Shugaban Ƙasa Na Gwamnan Bauchi Sun Bayyana
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Gargaɗi Magoya Bayan Wike A PDP

6 days ago
Ina Da Yaƙinin Tinubu Ne Zai Lashe Zaɓen 2027 — Wike
Siyasa

Ina Da Yaƙinin Tinubu Ne Zai Lashe Zaɓen 2027 — Wike

1 week ago
Ɗaukar Nauyin Ƴan Ta’addan Da Suka Farmake Mu A Kaduna Aka Yi – El-Rufai
Siyasa

Ɗaukar Nauyin Ƴan Ta’addan Da Suka Farmake Mu A Kaduna Aka Yi – El-Rufai

1 week ago
Next Post
Zaben 2023: INEC Za Ta Fara Bayyana Sakamakon Zaben Shugaban Kasa

Zaben 2023: INEC Ta Dage Bayyana Sakamakon Zaben Shugaban Kasa Zuwa Karfe 6 Na Yamma

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

September 8, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Kai Hare-hare 261, ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 1,950 A Watan Agusta – NOA

September 8, 2025
Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

September 8, 2025
'yansanda

An Kama Mutane 30 Da Zargin Laifin Aikin Dabanci A Yayin Zagayen Maulidi A Neja

September 8, 2025
Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

September 8, 2025
Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

September 8, 2025
Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

September 8, 2025
PDP

Jarin Da Sin Ta Zuba Kai Tsaye A Kasashe Cikin Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ya Karu Da Kashi 22.9% A 2024

September 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

September 8, 2025
Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

September 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.