• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Edo Da Ondo: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Gana Da Hukumar Zabe

byYusuf Shuaibu
2 years ago
Shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, ya na musabiha da sababbin kwamishinonin zaɓen da aka rantsar

Shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, ya na musabiha da sababbin kwamishinonin zaɓen da aka rantsar

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta gudanar da ganawa da manyan masu ruwa da tsaki a cikin harkokin zabe, kamar su jam’iyyun siyasa da kungiyoyin fararen hula da kuma manema labarai kan sabon yunkurin shirye-shiryen zaben gwamna a jihohin Edo da Ondo.

Wannan ita ce ganawa irinta ta farko tun bayan kammala zaben cike gurbi da ya gudana a watan Fabrairun 2024, a jihohi 26 da ke fadin kasar nan.

Babban makasudin taron shi ne, yadda za a samu nasarar gudanar da sahihin zaben gwamna a jihohin Edo da Ondo. Zaben gwamnan Jihar Edo zai gudana ne a ranar 21 ga Satumbar 2024, yayin da za a yi zaben gwamnan Jihar Ondo a ranar Asabar, 16 ga Nuwambar 2024.

Tuni dai jam’iyyu suka gudanar da zaben fitar da gwani na gwamnan Jihar Edo. A cewar jadawalin zaben, jam’iyyu suna da kwanaki 21 ne kacal wajen mika bayanan ‘yan takararsu ga hukumar zabe.

Shugaban hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, wanda ya jagoranci ganawar ya bayyana cewa hukumarsa ta horar da jami’an jam’iyyu na yankuna ta yadda za a taimaka wa dukkan jam’iyyun siyasan. Ya kara da cewa sun bude adireshin amsar bayanan ne tun a ranar 4 ga Maris, 2024, sannan kuma suka rufe da misalin karfe 6 na yamma na ranar Asabar, 24 ga Maris ta 2024.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

A cewarsa, bayan makonni biyu aka sake budewa saboda ba dukkan jam’iyyu suka saka bayyana ‘yan takaransu ba.

Hukumar INEC ta yi kira ga jam’iyyun siyasa su ci gaba da bin jaddawalin ayyukan zaben domin kaucewa rudadi.

Za dai a fara gudanar da zaben fitar da gwani na gwamnan Jihar Ondo a ranar 6 ga Afrilun 2024, wanda za a kammala a ranar 27 ga Afrilun 2024. A ciki jam’iyyun siyasa 19, 16 ne kadai suka nuna sha’awarsu ta shiga zaben.

Da yake jawabi, shugaban gamayyar jam’iyyu, Yusuf Dantalle ya bayyana cewa babu uzuri matukar an gaza gudanar da zaben gwamna a jihohin Edo da Ondo yadda ya kamata.

Jihohin Edo da Ondo dai kowannensu yana da kananan hukumomin 18. Yayin da Jihar Edo take da masu rajistar zabe guda 2,501,081, cibiyoyin zabe 192 da kuma rumfunan zabe 4,519, inda Jihar Ondo take da yawan masu rajistar zabe guda 1,991,344, cibiyoyin zabe 203 da kuma rumfunan zabe 3,933.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Next Post
bashi

Jihohin Nijeriya 10 Da Ke Kan Gaba A Yawan Bashi

LABARAI MASU NASABA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version