• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Edo Da Ondo: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Gana Da Hukumar Zabe

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Ku Nisanci Shiga Siyasa, Gargaɗin INEC Ga Sabbin Kwamishinoninta

Shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, ya na musabiha da sababbin kwamishinonin zaɓen da aka rantsar

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta gudanar da ganawa da manyan masu ruwa da tsaki a cikin harkokin zabe, kamar su jam’iyyun siyasa da kungiyoyin fararen hula da kuma manema labarai kan sabon yunkurin shirye-shiryen zaben gwamna a jihohin Edo da Ondo.

Wannan ita ce ganawa irinta ta farko tun bayan kammala zaben cike gurbi da ya gudana a watan Fabrairun 2024, a jihohi 26 da ke fadin kasar nan.

Babban makasudin taron shi ne, yadda za a samu nasarar gudanar da sahihin zaben gwamna a jihohin Edo da Ondo. Zaben gwamnan Jihar Edo zai gudana ne a ranar 21 ga Satumbar 2024, yayin da za a yi zaben gwamnan Jihar Ondo a ranar Asabar, 16 ga Nuwambar 2024.

Tuni dai jam’iyyu suka gudanar da zaben fitar da gwani na gwamnan Jihar Edo. A cewar jadawalin zaben, jam’iyyu suna da kwanaki 21 ne kacal wajen mika bayanan ‘yan takararsu ga hukumar zabe.

Shugaban hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, wanda ya jagoranci ganawar ya bayyana cewa hukumarsa ta horar da jami’an jam’iyyu na yankuna ta yadda za a taimaka wa dukkan jam’iyyun siyasan. Ya kara da cewa sun bude adireshin amsar bayanan ne tun a ranar 4 ga Maris, 2024, sannan kuma suka rufe da misalin karfe 6 na yamma na ranar Asabar, 24 ga Maris ta 2024.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

A cewarsa, bayan makonni biyu aka sake budewa saboda ba dukkan jam’iyyu suka saka bayyana ‘yan takaransu ba.

Hukumar INEC ta yi kira ga jam’iyyun siyasa su ci gaba da bin jaddawalin ayyukan zaben domin kaucewa rudadi.

Za dai a fara gudanar da zaben fitar da gwani na gwamnan Jihar Ondo a ranar 6 ga Afrilun 2024, wanda za a kammala a ranar 27 ga Afrilun 2024. A ciki jam’iyyun siyasa 19, 16 ne kadai suka nuna sha’awarsu ta shiga zaben.

Da yake jawabi, shugaban gamayyar jam’iyyu, Yusuf Dantalle ya bayyana cewa babu uzuri matukar an gaza gudanar da zaben gwamna a jihohin Edo da Ondo yadda ya kamata.

Jihohin Edo da Ondo dai kowannensu yana da kananan hukumomin 18. Yayin da Jihar Edo take da masu rajistar zabe guda 2,501,081, cibiyoyin zabe 192 da kuma rumfunan zabe 4,519, inda Jihar Ondo take da yawan masu rajistar zabe guda 1,991,344, cibiyoyin zabe 203 da kuma rumfunan zabe 3,933.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugabancin PDP: Yankin Arewa Ta Tsakiya Ya Dage Kan Cika Wa’adin Ayu

Next Post

Jihohin Nijeriya 10 Da Ke Kan Gaba A Yawan Bashi

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

7 days ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

1 week ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

1 week ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

2 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

2 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

2 weeks ago
Next Post
bashi

Jihohin Nijeriya 10 Da Ke Kan Gaba A Yawan Bashi

LABARAI MASU NASABA

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.