Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Zaben Kananan Hukumomi A Filato: APC Ta Razana -Kwamared Idris

by Tayo Adelaja
September 27, 2017
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Lawal Umar Tilde, Jos

Fargabar da Jam’iyyar APC ke yi a jihar Filato na ganin ba za ta yi nasara ba a zabubbuka masu zuwa a jihar ya sa ta kasa gudanar da zaben Kananan Hukumomi. Wannan furucin ya fito ne daga bakin Shugaban kungiyar ‘Transform Nigeria Group {TNG}’ tya matasa, karkashin jam’iyyar PDP, rashen jihar Filato, Kwamared Idris Zahiru Umar a lokacin da yake tattaunawa da Wakilinmu a kwanakin ba ya.

samndaads

Ya ce jihar Filato jiha ce ta jam’iyyar PDP, tun dawowar gwamnatin Dimokurdiyya har yanzun nan tana da karfi a kowane lungu na jihar.

Kwamared Umar, wanda ya ce a zaben 2015, jam’iyyarsu ta PDP ta lashe kujerun Senatoci Uku da na ‘yan Majalisar wakilai na Tarayya Shida, da ‘yan Majalisar Dokoki na jihar guda goma sha uku. Ya ce hangen Dala ne kawai mutanen jihar suka yi wa jam’iyyar APC, ya sa suka zabeta, amma a shekaru biyu din nan da Gwamnan ya yi a ofis ya nuna masu a fili sun yi zaben tumun dare.

Shugaban ya ce, rikicin da ya addabi uwar jam’iyyar na kasa babban darasi ne da ya karantar da dukkan ‘yan jam’iyyar, wanda hatta tsohon Shugaban, kasa GoodLuck Jonathan, a wani taron jam’iyyar da aka gudanar a Abuja ya amince cewa an yi kuskure, kuma ya ce a zabubbuka masu zuwa na 2019, dan takarar shugaban na jam’iyyar zai fito ne daga Arewa, wanda ya ce hakan zai baiwa jam’iyyar dama ta kafa gwamnati .

Daga nan sai Zahiru Umar ya yi amfani da wannan damar wajen kira ga ’yan jam’iyyar don zabar shugabanni nagari da za su jagoranci al’ummar kasar nan cikin nasara. Ya ce mutane irin su Barista Tanimu Turaki ne suka cancanta a zaba su shugabanci kasa a 2019. Ya ce domin ya yi an gani a lokacin da yake rike da mukamin Minista.

SendShareTweetShare
Previous Post

Jam’iyyar APC Ta Shirya Taro Kan Jin Ra’ayoyi

Next Post

Dokokin Hukunta Masu Aikata Laifukan Zabe A Nijeriya!

RelatedPosts

A duniyar Nijeriya ta yanzu, da yawan mutane da ma masu lura da al’amuran yau da kullum su na kallon gudanar da zabukan kananan hukumomi

Abubuwan Al’ajabi A Zaben Kananan Hukumomin Kano

by Sulaiman Ibrahim
5 hours ago
0

Kuri’un Da Aka Kidaya Sun Haura Na Zaben Gwamna A...

Ranar Bude Makarantu

Korona: Har Yanzu Babu Ranar Bude Makarantu A Jihar Kaduna

by Sulaiman Ibrahim
5 hours ago
0

 Dukkanin makarantun Firamare da na sakandari da suke jihar Kaduna...

Kwalejin Kimiyya

Gwamnatin Tarayya Za Ta Gina Kwalejin Kimiyya Ta Farko A Borno

by Sulaiman Ibrahim
5 hours ago
0

Ranar Litinin Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya kai...

Next Post

Dokokin Hukunta Masu Aikata Laifukan Zabe A Nijeriya!

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version