• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Kananan Hukumomi Ko Dai Shiririta?

by Leadership Hausa
11 months ago
in Manyan Labarai
0
Yaya Kuri’un Yankin Arewa Maso Yamma Za Su Kasance A 2023?

A woman votes at a polling station in Kano, Nigeria, March 28, 2015. Many Nigerians fear a clash along religious, ethnic, and sectional lines regardless of the result of the presidential race between incumbent Goodluck Jonathan, a Christian from the south, and Muhammadu Buhari, a former military ruler and Muslim northerner. (Samuel Aranda/The New York Times)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A zabubbukan kanannan hukumomi na kwanakin baya, da aka gudanar a wasu jihohin kasar nan, gwamnonin jihohin, sun yi ta hakilon yin karfakarafa domin ganin cewa, ko ta halin kaka, sai ‘yan takararar su ne, suka lashe zabubbukan.

Misali a makonni ukun da suka gatabata, an gudanar da zabubbukan kanannan hukumomi a jhohin Anambra, Kwara, Kebbi, Ribas, Biniwe, Akwa Ibom, Filato da dai, sauransu.

  • Me Najeriya Za Ta Iya Samu Daga Tsarin BRICS?
  • Me Najeriya Za Ta Iya Samu Daga Tsarin BRICS?

Hakazalika, ma jihohin Kano da Kaduna, suna ci gaba da kai gwauro su kai mari, domin ganin sun dora ko nada ‘yan takarar jam’iyyunsu a zabubbukan shugagannin na kanannan hukumomin.

Hukumomin gudanar da zabubbukan na kananan hukumomi masu zaman kansu na jihohin da kundin tsarin mulki kasar na shekarar 1999 da aka sabunta, ya dora masu alhakin gudanar da dabubbukan bisa adalci.

Sai dai, kuma abin takaici, akasarin zabubbukan na kanannan hukumomin da aka gudanarwa, cike suke da tabka magudin da kusan ma ya wuce hankali.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

Hakanan ma, wani da ya zama tamkar gari a yayin gudanar da zabubbukan na kanannan hukumomi a kasar shi ne, yadda jam’iyyar da ke rike da madabun iko a jihohin, galibi ‘yan takararta ne, suke lashe zabubbukan, kusan tun daga na shugaban karamar hukuma har zuwa na Kansiloli.

Sai dai kuma, an samu wani dan karamin sauyi a jihar Akwa Ibom, inda jam’iyyar adawa ta APC, ta lashe zaben karamar hukuma daya kacal a jihar.

An dai sha zargin gwamnonin jihohin wajen yin amfani da ‘yan korensu don yin karfa-karfar tabka magudin zabe.

Misali, a jihar Ribas, a zabubbukan kanannan hukumomi na jihar da aka yi bada dadewa ba, an zargi gwamnan jihar Siminalayi Fubara da tabka irin wannan kazamin magudin, zaben, inda jam’iyyar APP da goyawa baya a lokacin zaben, ta samu gaggarumar galaba, a kan sauran jam’iyyun adawa da suka fafata a zaben.

Jam’iyyar ta APP ta lashe zabubbukan ne, saboda goyon bayan da ta samu daga gun gwamna Fubara, ta hanyar nada masu yi masa biyayya a matsayin jami’an hukumar zaben jihar da suka gudanar da zabukan.

Bugu da kari kuma wadannan jami’an hukumar zaben, sun samu sahalewar ‘yan majalisar dokokin jihar da Fubura ke juya su kamar Waina, don su gudanar da zabubbukan tun daga Kujerar shugabannin kananan hukumimin har zuwa Kujerar Kansilpli.

A irin wadannan zabubbukan, cike suke da magudi da abin al’ajabi, domin tun kafin ma a sanar da sakamkon zabukan, aka fara taya ‘yan takarar jam’iyya mai mulki, murnar lashe zabe.

Yana da kyau a gane lamarin, duk da cewa, irin yakin da kanannan hukumomin kasar suka sha fama suna yi, na sai sun samu ‘yancin cin gashin kansu, wanda daga bisani, suka yi nasara bayan da kotun kolin kasar ta yanke hukuncin ba su damar cin gashin ‘yancin kansu, amma ga dukkan alamu, har yanzu kusan yakin bai kare baa kwai sauar rina a kaba.

Idan har yanzu ba a samar da tsarin gudanar da sahihan zabubbukan a kanannan hukumomi ba, idan aka lura da yadda gwamnonin jihohin ke yin amfani da dukkan karfin ikon da suke da shi don ganin ‘yan takarar jam’iyyun su, sun samu nasara, to za a iya cewa, tamkar an kashe Maciji ne, amma ba a sare kansa ba.

Amma domin a kawo karshen irin wannan kwamacalar a zabubbukan kanannan hukumomi, wannan jaridar, na son kara jaddada kiranta na a soke hukumomin gudanar da zabe masu zaman kansu na jihohi.

Maimakon haka ma sai a bar hukumomin zaben su rinka gudanar da zabubbuka, kamata ya yi a bai wa hukumar zabe maizaman kanta ikon gudanar da zabukan.

Irin wannan tabka magudin da dagewar da gwamnonin jihohin suke yi, na sai ‘yan takarar jam’iyyunsu sun lashe zabubbukan, ba zai sakarwa da shugabanninta mara ba don yiwa al’umomin su aiki, kamar yadda ya kamata ba.

Abin takaici ne, sai da goyon bayan gwamna ne, kawai dankarar kujerrar shugaban karamar hukuma ko kuma ta Kansila zai iya lashe zabe tare da amincewar wasu daga cikin jiga-jigan shugabannin jim’iyya mai ci.

Bugu da kari kuma, akasarin Kansilolin da suka lashe zabe, idan shugaban karamar hukumar ya aikata laifin da ya cancanci a tsaige shi, ba su da wani ikon iya tsige shi.

Duk wani darasin da aka koya na bai wa hukumomin zabe masu zaman kansu na jihohin kasar nan ragamar gudanar da zabubbukan, hakan na ci gaba da nuna cewa, har yanzu wadanda aka zaba a matsayin shugagabannin kanannan hukumomin, na ci gaba da kasancewa ‘yan amshin Shata ne, wato za su ci gaba da kasancewa ne a karkashin ikon gwamnonin saboda tsayuwar da suka yi tsayin daka, wajen ganin shugabannin, sun lashe zabubbukan, wanda kuma a dole ne, sai sun bi umarnin gwamnonin

Lamarin dai, babban abin kunya ne a harkar dimokiradaiyyar kasar nan musamman ma ganin yadda gwamnonin, ke yin amfani da hukumomin gudanar da zabubbukan jihohinsu, don su tabka magudin zabe, wanda kuma haka ne ke nunawa a zahiri cewar, zabubbukan tamkarwata shiririta ce kawai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ShiriritaZaben Kananan Hukumomi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Taron BRICS Na Wannan Karo Ya Shaida Himmar Kasashe Mambobin Kungiyar Wajen Ingiza Zaman Lafiya A Duniya

Next Post

Rikita-rikitar Aikin Hanyar Abuja Zuwa Kaduna…

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

3 hours ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

8 hours ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da É—umi-É—uminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

11 hours ago
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

13 hours ago
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
Manyan Labarai

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

17 hours ago
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
Manyan Labarai

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

18 hours ago
Next Post
Rikita-rikitar Aikin Hanyar Abuja Zuwa Kaduna…

Rikita-rikitar Aikin Hanyar Abuja Zuwa Kaduna...

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin HaÆ™ar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin HaÆ™ar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.