ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Kano: Alkali Na Fuskantar Tuhuma Kan Kuskuren Da Aka Tafka

by Abdullahi Muh'd Sheka
3 years ago
Kano

Yayin da jama’a ke nuna rashin jin dadinsu kan hukuncin da wasu alkalan kotunan daukaka kara suka yi a kan zaben Gwamnan Jihar Kano, majalisar kula da shari’a ta kasa (NJC) ta fara daukan matakai kan wannan lamarin.

Na farko daga cikin alkalan da suke fuskantar tuhuma daga NJC shi ne, mai shari’a Moore Aseimo Abraham Adumein na kotun daukaka kara wanda ya zartar da hukunci mai cike da ce-ce-ku-ce a shari’ar gwamnan Jihar Kano.

  • Gwamnatin Kaduna Ta Kaddamar Da Kwamitin Mutum 8 Don Inganta Harkokin Aikin Hajjin 2024
  • Da Dumi-dumi: Kotun Daukaka Kara Ta Ayyana Ranar Yanke Hukunci Kan Kujerar Gwamnan Adamawa

LEADERSHIP ta ruwaito cewa mai shari’a Adumein yana fuskantar tuhuma saboda gazawarsa wajen ganowa da kuma kyara kura-kuran rubutun da aka yi a shari’ar Gwamnan Jihar Kano.

ADVERTISEMENT

Wata majiyar ta ce da yawa daga cikin ‘yan Nijeriya sun yi korafi kan hukuncin shara’ar gwamnan Kano, wanda har yanzu suke bukatar yi musu bayanin yadda aka samu kura-kuran.

“Yawancin ‘yan Nijeriya da ke magana a kan hukuncin ba su karanta ba. Kuskuren da aka samu a hukuncin ya nuna karara kuskure ne na alkali amma ba na yi masa uzuri ba, dole ne ya amsa kuskurensa saboda jahilci ba uzuri ba ne a shari’a, dole ne ya fuskanci hukunci a wuyansa.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

“Kuskuren wannan hukuncin ya fito ne daga magatakarda wanda ya yi aiki a kai. Alkalin bai karanta karshen hukuncin ba bayan da sakatare ya yi aiki a kai. Alkalin da sakataren da suka yi aiki a kai dole ne su fuskanci hukunci,” in ji majiyar.

Majiyar ta ci gaba da cewa a bangaren shari’a tafka kuskure babban abin kunya ne ba kamar sauran sass aba, shi ya sa kuskure ke zama babban laifi idan an aikata a bangaren.

Ya ce NJC ba ta kare alkalan ta da aka samu da laifin ko kuma kuskure wajen gudanar da aiki. Majiyar ta ce, “Kusan kashi 98 cikin 100 na koke-koken da ake yi wa alkalan ana gudanar da bincike sannan idan aka same su da laifi za a iya dakatar da su ko kuma a kore su daga aiki.

“Majalisar NJC tana biyan dukkan alkalan tarayya albashinsu, shi ya sa muke samun horo idan aka same su da laifi. NJC kamar kotu ce ga alkalai, saboda masu korafi da alkalai suna wakiltar lauyoyi ne, inda ake tafka muhawara a dukkan wasu batutuwa.

“Bayan sun saurare su, za su yi watsi da bukatar ko kuma su sanya wa alkali takunkumi, ya danganta da hujjar da aka gabatar. Yawancin shari’o’in da ake yi wa alkalan a NJC daga kotun daukaka kara suke tasowa.” In Ji majiyar

Kano
Abdullahi Muh'd Sheka
+ postsBio
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Sakamakon Matsin Lambar Jami’an Tsaro, ‘Yan Ta’adda Na Fuskantar Ƙarancin Abinci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Kisan Gillar Mutum 7 A Kano: Sarakuna Da Malamai Da Iyaye Sun Nemi A Gaggauta Yanke Wa Waɗanda Ake Zargi Hukunci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

MASU ALAKA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
Next Post
FUDMA Za Ta Karrama Sarkin Bichi, Sarkin Daura Da Tsohon Gwamnan Katsina

FUDMA Za Ta Karrama Sarkin Bichi, Sarkin Daura Da Tsohon Gwamnan Katsina

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Kano

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Kano

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.