• English
  • Business News
Friday, May 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zagayen Maulidin Annabi (SAW) Ya Gudana Cikin Armashi A Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Rahotonni
0
Zagayen Maulidin Annabi (SAW) Ya Gudana Cikin Armashi A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamar kowace shekara, a bana ma al’ummar Musulmai masoya Annabin Tsira, Annabi Muhammad sun fito domin yin zagayen gari domin nuna murna da zagayowar ranar haihuwar Annabi Muhammad (SAW) a cikin garin Bauchi.

Zagayen Maulidin na bana ya kayatar ya kuma samu armashi kana an gudanar da shi lafiya ba tare da wani tashin hankali ko kalubale ba.

  • Maulidi: Duk Wata Wayewa Da Ba Koyi Da Manzon Allah Za Ka Ga Wauta A Cikinta – Sheikh Isma’il

Wakilinmu ya labarto cewa tun safiyar ranar Lahadi ne dai al’ummar musulmai, da kungiyoyin addini, gami da mawaka da sassan masoya Annabin suka fito domin yin wannan jerin gwanon da aka saba gudanarwa duk shekara cikin ado, kwalliya, fareti, wakokin yabon Manzo da sauransu.

Kamar yadda aka saba, dandamin filin kwallo na Kobi shine ke zama mikatin Maulidin a duk shekara kuma makarantun Islamiyoyi ne ke fara shiga sawu, inda ake fita bisa layi tare da nizami, haka a bana ma zancen ya gudana, inda masu maulidin suka taso daga Kobi, suka nausa kofar Fadar Sarkin Bauchi, Dakta Rilwanu Sulaiman Adamu inda suke mika masa gaisuwar Maulidin yayin da shi kuma ke saman fadarsa zaune na amsar gaisuwar.

Maulidin Annabi
Baya ga hakan, masu zagayen sun nausa zuwa titin Santaral, suka nufi titin Kofaran da zarcewa Bakin Kura, zuwa Tashan Babiye kana layin ya wuce zuwa titin Wunti da sauran manyan hanyoyin jihar dukka domin nuna farin ciki da wannan ranar ta Maulidi.
A gefe daya, masu maulidin kan raba kyautuka da alawa da fulawowi ga masu kallonsu, a yayin da su masu kallon ke mika kyautuka ga wadanda suke kan sahun Maulidin. Inda zagayen ke kara dankon kauna da fahimtar juna a tskanin bangarori daban-daban.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

Da muke zantawa da daya daga cikin malaman addinin musulunci kuma almajirin Sheikh Dahiru Usman Bauchi, Malam Muhammadu Sunusi, ya bayyana cewar suna fitowa zagayen Maulidin ne domin nuna kauna da soyayya ga Annabi Muhammad (S), har ma ya ce zagayen na baya ya kayatar sosai.

“Alhamdullahi zagayen baya sai godiya wa Allah domin an samu sauye-sauye da gyare-gyare da suka kara inganta zagayen na bana.
“Muna fitowa zagayen Maulidin nan ne domin Allah domin Annabi (S), ka ga dai da idonka babu wani abun da ake yi da aka daina, maza da mata, yara da kanana, tsoffi kowa ya fito domin nuna murnarsa da zagayowar wannan ranar kuma cikin tsari.

Maulidin Annabi
“Kuma abun da ake yi dai shine aka saba, wato raya yabon Manzon Allah (SAW), nuna soyayayarsa da tunawa ma jama’a Manzon nan da yaren labaranci, Hausa ga wasu ma da sifa da shiga irin na Yarbawa da Inyamurai wasu Fulani haka aka kayatar da wunin nan gaba daya tun safe har dare Manzon Allah ake anbato a jihar nan domin duniya ta shaidi mun yi wa Allah godiya a kan wannan ni’ima da ya yi mana.”

Malamin ya ce godiya ne suke yi da ni’imar da Allah ya musu, yana mai cewa babu wata ni’ima da ta kai samun Manzon Allah.
“Don haka muka fito domin nuna godiya da wannan ni’ima, da rahama da aka samu sakamakon zuwan Manzon Allah.”

Sunusi wanda ake wa lakabi da fiya-fiya, ya kuma nuna cewa an yi taron lafiya an kammala lafiya don haka ne suke kara godiya ga Allaha kan hakan, “Masu sukar Maulidi ya kamata zagayen da ake yi ya zama musu wa’azi na cewa ya kamata su daina domin hakan ba ya rage komai sai kara armashi wa Maulidi.”
Muhammadu Sunisi ya yi fatan Allah maimaita kana ya nuna gamsuwarsa da yadda aka yi tsari masu kyau wajen gudanar da maulidin cikin kwanciyar hankali da annashuwa.

Maulidin Annabi
Shi ma da yake zantawa da ‘yan jarida kan wannan zagayen, wakilin ‘yan uwa musulmai Almajiran Sheikh Zakzaky a jihar Bauchi, Malam Ahmad Yusuf Yashi, ya yi amfani da wannan damar wajen kira ga jama’a da su dauki maulidi a matsayin babban alamin hadin kai da inganta zaman lafiya a tsakanin jama’a.

“Kamar kowace shekara a bana ma ranar 12 ga watan Rabi’u Auwal mun fito ne domin nuna farin ciki da zagayowar ranar haihuwar Manzon Rahma, Muhammadu Dan Abdullahi (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi), kuma alhamudullahi ba mu kadai ma al’umma gata nan gabaki daya an fito domin yin musharaka wajen nuna wannan farin cikin.

“Sakona a irin wannan rana shine cewa mu yi amfani da wannan dama wajen dinke baraka a tsakanin al’ummar musulmai, duk da banbance-banbancen da ke akwai, tun da Manzon Allah ya hadamu, Kaaaba ta hadamu mu yi amfani da wannan damar mu zauna mu dinke mu zama abu guda domin cigaban al’ummar musulmai da jama’a gabaki daya,” Inji Yashi.

Maulidin Annabi
A sakonsa na fatan alkairi ga masu zagayen Maulidin, Sarkin Bauchi, Dakta Rilwanu Sulaiman Adamu ya nuna farin cikinsa kan yadda zagayen na bana ya gudana cikin kwanciyar hankali da armashi, sai ya yi kira kan kara hada kai da fahimtar juna a tsakanin al’umma domin rayuwa take ingantuwa a jihar.

Ya kuma yi fatan Allah maimaita tare da taya al’umma murnar zagayowar wannan maulidin na 2022.
A sakonsa na ranar Maulidi da gwamnan Bala Muhammad ya fitar, ya taya al’ummar musulmai murnar zagayowar ranar Maulidi tare da rokonsu da su kasance masu koyi da dabi’un Manzo.

A sakon da ya fitar ta hannun kakakinsa, Muktar Gidado, gwamnan ya ce dukkanin rayuwar Manzon Allah abin koyi ne ga al’umma, kuma a cewarsa, Annabi ya koyar da zaman lafiya, kwanciyar hankali, kyauta, Dabi’u na kwarai, don haka ne ya nemi al’umma da su yi koyi domin kyautata zaman lafiya a jihar da kasa baki daya.

Gwamnan ya yi fatan cewa jama’a za su yi addu’ar zaman lafiya da kwanciyar hankali ga kasa a yayin da suke gudanar da shagulan bikin Maulidi na bana.

Daga bisani ya yi fatan cewa za a gudanar da taron Maulidin a ciki da wajen jihar lafiya kamar yadda aka fara cikin kwanciyar hankali. Sanann, ya nemi jama’a da su kara yi wa gwamantinsa addu’a domin ta cimma nasarorin da ta sanya a gaba.

Shi kuma Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya bukaci jama’a da su yi addu’ar samun shugabanni na kwarai da gudanar da zaben 2023 cikin kwanciyar hankali.

Da yake jawabi a wajen taron Maulidin da ya saba shiryawa na bana, Dahiru ya ce suna gudanar da Maulidin ne domin raya ranar da aka haifi Manzon Allah (SAW), ya kuma jawo hankalin al’umma da su cigaba da koyi da halayen Manzon Allah a kowani lokaci.

Maulidin Annabi
Shi kuma a jawabinsa a wajen taron Maulidin Manzon Allah da Sheikh Dahiru Bauchi ya shirya, gwamnan Jihar Bala Muhammad ya ce juriya, sadaukarwa, zaman lafiya, taimako da neman ilimi na cikin ababen da Manzon Allah ya koyar da sahabban sa masu daraja, don haka ne ya nemi al’umma da su yi koyi.

Gwamna Bala Muhammad ya bukaci Malamai da su daina sukar shugabanni a gaban dalibansu ba tare da kwararan hujjoji ba domin kyautata rayuwa a kowani lokaci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Matakan Dakile Annobar Ambaliyar Ruwa (Ra’ayinmu)

Next Post

Na Amince Zan Goyi Bayan Takarar Atiku Abubakar —Wike

Related

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

1 month ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

1 month ago
An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
Rahotonni

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

1 month ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Rahotonni

Amurka Ta Sayi Kayayyakin Nijeriya Na Dala Miliyan 643 A Wata 2 – Rahoto

1 month ago
Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi
Rahotonni

Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi

1 month ago
Tinubu
Manyan Labarai

Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027

2 months ago
Next Post
Na Amince Zan Goyi Bayan Takarar Atiku Abubakar —Wike

Na Amince Zan Goyi Bayan Takarar Atiku Abubakar —Wike

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

May 23, 2025
Sin Da ASEAN Sun Kammala Tattaunawa Game Da Kafa Yankin Ciniki Cikin ‘Yanci

Sin Da ASEAN Sun Kammala Tattaunawa Game Da Kafa Yankin Ciniki Cikin ‘Yanci

May 23, 2025
An Gudanar Da Taron Kolin Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Na Duniya Na Shekara Ta 2025 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kolin Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Na Duniya Na Shekara Ta 2025 A Beijing

May 23, 2025
Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3

Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3

May 23, 2025
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

May 23, 2025

Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba

May 23, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Gwamnatin Jamus Friedrich Merz

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Gwamnatin Jamus Friedrich Merz

May 23, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

May 23, 2025
Shugaban Kasar Sin Ya Jaddada Muhimmancin Samun Ci Gaba Mai Inganci Ta Fuskar Raya Wayewar Kai

Shugaban Kasar Sin Ya Jaddada Muhimmancin Samun Ci Gaba Mai Inganci Ta Fuskar Raya Wayewar Kai

May 23, 2025
Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?

Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?

May 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.